Search This Blog

Friday, 27 January 2023

Sabon Kudi: Ganduje ya tausaya wa jama'a, ya kuma yi kira da a tsawaita wa'adi


Gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya jajanta wa al'ummar jihar kan wahalhalun da ake fama da su a sakamakon manufofin gwamnatin jihar. sabuwar manufar babban bankin Najeriya (CBN) kan sake fasalin kudin naira wanda ya fara yaduwa a makon jiya.

Kwamishanan yada labarai na jihar Malam Muhammad Garba, wanda ya bayyana hakan cikin wata sanarwa a ranar Juma'a, ya ce gwamnati ba ta ji dadi ba matuka bisa ga sakamakon da aka samu na wannan manufa da ke shafar al'umma musamman talakawan Najeriya saboda lokacinta da kuma gajeren lokacin mika mulki.

Malam Garba ya bayyana cewa Gwamna Ganduje ya bayar da tabbacin cewa gwamnatin jihar na bakin kokarinta na hada kai da sauran masu ruwa da tsaki. duba da tsawaita wa'adin da aka sanya domin janye tsofaffin gaba daya tare da bayar da isassun kudade ga al'umma.

Kwamishinan ya kara da cewa, yayin da gwamnati, da mafi yawan 'yan Najeriya , sun yi imanin cewa jama’a na fuskantar wahalhalu sakamakon sake fasalin kudin Naira, ya kuma yi kira ga babban bankin CBN da ya kara wa’adin da aka sanya na aiwatar da manufofin.

Akan karancin man fetur da ake fama da shi, sanarwar ta kuma bukaci kamfanin man fetur na Najeriya (NNPC) ) domin tabbatar da wadata da rarraba shi ga 'yan Najeriya.

Gwamnan ya bukaci jama'ar jihar da su kwantar da hankalinsu domin daukar matakin da ya dace domin gyara al'amura.

Yanzu-yanzu: Kotu ta bayyana Oyetola a matsayin Gwamnan Osun Gwamna, ta kori Adeleke

Kotun sauraren kararrakin zabe ta Osun da ke zamanta a Osogbo, babban birnin jihar Osun a ranar Juma’a ta bayar da umarnin a janye takardar shaidar cin zabe da aka baiwa gwamnan jihar, Sanata Ademola Adeleke ba tare da bata lokaci ba.

Alkalin kotun mai shari’a Tertsea Kume a lokacin da yake karanta hukuncin a Osogbo, ya bayyana cewa gudanar da zaben bai dace da dokar zabe ba.

Mai shari’a Kume ya bayyana cewa, an kada kuri’a a rumfunan zabe shida a lokacin zaben, ya kuma ci gaba da cewa, bayan da aka cire sahihin kuri’un da aka kada a wadannan rumfunan zabe, Adegboyega Oyetola na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ya samu kuri’u 314,941 yayin da jama’ar kasar suka samu kuri’u 314,941. Jam'iyyar PDP Ademola Adeleke ya samu kuri'u 290,266.

Malamai Da Tsofaffin Soji Ba Sa Kwazo A Jagoranci —Obasanjo

Tsohon Shugaban Kasa, Cif Olusegun Obasanjo, ya ce galibi ba a samun wani ci gaba na a zo a gani a jihohin da suka kasance karkashin jagorancin malamai ko tsofaffin soji.

Obasanjo ya ce babu wani ci gaban da aka samu a jihohin kasar nan da ke karkashin jagorancin mutane masu rike da matsayin Farfesa ko Dakta da tsoffin sojoji, har ma da malaman makarantu.


Tsohon Shugaban na Najeriya na wannan furuci a jawabinsa yayin wani taro kan zurfafa al’adun dimokuradiyya da aka gudanar ranar Alhamis a Fatakwal, babban birnin Jihar Ribas.

Obasanjo ya ce duk da yake an samu wasu jajirtattun shugabannin da ba su da yawa, akasarinsu ba sa iya mulki mai kyau saboda rashin samun mataimaka na gari, abin da ke hana su jagorancin da ake bukata.
A cewarsa, rashin tattaunawa tsakanin shugabannin da masu taimaka musu, kan haifar da gibi wajen musayar ra’ayi, matakin da ke hana samun fahimtar juna da hadin-kai wajen cimma manufar ci gaba da ake bukata.

Obasanjo ya ce, bayan kwashe shekaru 60 da samun ‘yancin kan Najeriya, har yanzu shugabannin kasar sun kasa samar da yanayin shugabanci mai inganci wanda zai samar wa kasar ci gaba da kuma magance banbance-banbancen da ake samu na kabilanci da addini da kuma shiya.

Obasanjo ya ce, yadda ake tafiyar da dimokuradiyyar Najeriya ya haifar da rabe-raben kawuna da mummunar alaka da rashin amince wa juna da kuma rashin kishin kasa a tsakanin jama’a da kuma al’umma a sassan kasar.

Obasanjo ya ce, abin takaici ne yadda karya da zage-zage da son kai suka mamaye yakin neman zaben da ake gudanarwa yanzu haka, maimakon gabatar da shirin da ake da shi na gina kasa.


A halin yanzu dai jihohin Borno da Cross Rivers ne kawai ke da masu rike da mukamin Farfesa da ke jagorancin su a matsayin gwamnoni, yayin da ake da wasu masu mukamin Dakta.
AMINIYA 

2023PDP Ce Ta Haifar Da Wahalar Man Fetur A Najeriya – Tinubu


Dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu ya ce dillalan man da PDP ta bai wa lasisi zamanin mulkinta ne ke boye fetur yanzu a Najeriya.

Tinubu ya kuma ce magoya bayan PDPn da jam’iyyar ta bai wa lasisin zamanin mulkinta ne ke yin hakan saboda dalilan siyasa da kuma haddasa dogayen layuka a gidajen mai.

Idan muka je saro kaya da tsoffin kudi ba a karba – ’Yan kasuwar Gombe
‘Duk Shugaban Kasar da zai zo zai fuskanci kalubale irin na Jonathan da Buhari’
Tinubu ya bayyana hakan ne yayin gangamin yakin neman zabensa da ya gudanar a Jihar Binuwai ranar Alhamis.

Ya ce, PDP Jam’iyya ce ta ruruta wutar talauci ce, musamman idan aka yi la’akari da yadda ’yan Najeriya ke shan bakar wahala a yanzu.


Sun bai wa magoya bayansu lasisin da yanzu ya haifar da dogayen layuka na jabu a gidajen mai. PDP haka ya ishe ku fa!”

Ya kuma ce rashin sanin doka ne ya sanya abokin hamayyarsa, Atiku Abubakar, ya ce kasuwancin sufuri yake a lokacin da yake aiki da Hukumar Hana Fasakwauri ta Kasa, lokacin da yake amsa tambayar da wasu suka yi masa kan yadda ya yi arziki haka.

“Suka tambaye shi ya aka yi ya yi arziki da yake da shi, sai ya kada baki ya ce kasuwancin sufuri yake. Bai san cewa laifi ne babba ba a ce kana ma’aikacin gwamnati kuma ka yi wani aikin ba noma ba,” in ji Tinubu.
Tsohon Gwamnan Jihar Legas din ya kuma ce yana da yakinin yadda ya ciyar da jiharsa gaba lokacin da ya jagoranceta, zai tabbatar ya yi wa Najeriya haka.
AMINIYA 


Thursday, 26 January 2023

Babban Bankin Najeriya Ya Ce Ya Kashe Dalar Amurka Biliyan 11.42 Don Farfado Da Darajar Naira

Rahoton da babban bankin Najeriya ya fitar a shafinsa na yanar gizo ya ce bankin ya kashe dalar Amurka biliyan 11.42 a cikin watanni 7, daga watan Janairu zuwa watan Yuli na shekarar 2022 domin a farfado da darajar naira.

Masana tattalin arziki da kwararru a fannin hada-hadar kudi na ganin wannan kokari da bankin CBN ya yi bai hana matsalar canji tsakanin dalar Amurka da naira ba, hasali ma har yanzu farashin kayan masarufi na karuwa a kasuwanni.

Ya zuwa wannan lokacin, ana sayar da dalar Amurka daya a kan naira 750 a kasuwar bayan fage yayin da a banki kuma ake sayar da dalar kan naira 450, bambancin naira 300 kenan tsakanin banki da kasuwar bayan fage.

A hirar shi da Muryar Amurka, Umar Garkuwa, daya daga cikin manyan ‘yan canjin kudi a Abuja babban birnin tarayyar Najeriya, ya ce karyewar naira laifin babban bankin kasar ne ba laifin ‘yan canji ba.

Garkuwa ya ce matsalolin harkar canji a Najeriya ba kamar a wasu kasashen duniya ba ne, domin lamarin ya zama wata harka da wasu ‘yan kasar da kuma CBN suke amfani da ita wajen azurta kansu. Ya kara da cewa, kasuwar canjin kudin kasashen waje a Najeriya dabam ta ke kuma babu yadda za a magance 

A lokacin da shugaba Mohammadu Buhari ya karbi mulki ana canza dala daya akan naira 184 zuwa 185 amma yanzu ana sayen dala daya a kan Naira 750, a cewar Garkuwa.

A lokacin da ta ke bayani kan yadda canjin kudi ya shafi farashin kayayyaki a kasuwa, Madam Elizabeth Sudan, ta bayyana cewa, kudin kaya a kasuwanni ya karu, domin a kwanakin baya ta sayi fakitin sinadarin Maggi na dandanon miya kan naira 750 amma ya koma naira 800, buhun shinkafa ya tashi daga dubu 40 zuwa dubu 44, kuma ko ina aka je sai a ce dalar Amurka ta yi tsada.

A nashi bayanin, masanin tattalin arziki Yusha'u Aliyu, yana ganin akwai matsalar da ya kamata a magance idan bankin CBN ya kashe wadannan kudaden kuma darajar naira ba ta hau ba.
VOA 

Wednesday, 25 January 2023

Take-Taken Da Ake Nufi Da Karancin Mai Da Sauya Fasalin Naira —Tinub

Dan takarar Shugaban Kasa karkashin Jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu, ya yi zargin matsalar karancin mai da ake fuskanta da sauya fasalin wasu takardun Naira da aka yi, take-taken neman wargaza Zaben 2023 ne kawai.

Tinubu ya bayyana haka ne yayin gangamin yakin neman zaben APC da ya gudana ranar Laraba a Abeokuta, babban birnin Jihar Ogun.

Na tafka kuskure a tafiyar Buhari, ba zan maimaita da Tinubu ba — Naja’atu
Muna da hujjoji kan cewa Tinubu tsohon mai laifi ne – Dino Melaye 
“Ba sa son zaben ya gudana. So suke su wargaza shi. Za ku bari hakan ta faru?, in ji Tinubu.

Dan takarar ya ce yana da yakinin matsalar karancin fetur ba za ta hana ’yan Najeriya zuwa kada kuri’a ba ranar zabe.


“Sun fara bullo da batun ‘babu mai, kar ku damu, idan babu mai za mu taka da kafa zuwa wajen zabe.

“Idan kun ga dama ku kara kudin mai, ko boye man ko kuma ku canza wa naira launi, za mu ci zabe,” in ji shi.

Har Yanzu Ban Taba Ganin Sabbin Takardun Naira Ba- Gwamna Ortom

Gwamna Jihar Benuwe, Samuel Ortom, ya bayyana cewa duk da matsayinsa na mai rike da mafar iko amma har yanzu bai taba hada ido da sabbin takardun Naira ba.

Mista Ortom ya bayyana hakan a wannan Larabar yayin da yake kira ga mahukunta da su tsawaita wa’adin amfani da tsofaffin takardun kudin kasar.

Gwamnan ya bayyana damuwa dangane da karancin wa’adin amfani da tsohuwar naira da aka bai wa ’yan Najeriya, yana mai jan hankali da a yi la’akari da mazauna karkara da ba su da masaniyar abin da ke faruwa dangane da sauya wa takardun kudin fasali.

Aminiya ta ruwaito cewa, Gwamnan ya yi wannan koke ne a jawabinsa yayin ziyarar da Majalisar Gudanarwa ta Jami’ar Sarwaaun Tarka ta kai Fadar Gwamnatin Benuwe da ke birnin Makurdi.

A cewarsa, ­“a matsayina na Gwamna, har yanzu ban yi ido biyu da sabbin takardun Naira ba duk da cewa kwanaki shida kacal suka rage wa’adin amfani da tsohuwar naira ya cika.

“Yanzu a irin wannan yanayi ya za a karke ke nan da mazauna karkara?

“Ina goyon bayan kiran da Majalisar Dattawa ta yi na a tsawaita wa’adin amfani da tsofaffin takardun naira.

“Tun ba a je ko’ina ba jama’a sun fara shiga mawuyacin hali doriya a kan na matsalar tsaro da suke fuskanta.


“Jama’a suna cikin kunci, lamurra sun tabarbare saboda komai ba ya tafiya a kan tsari, kuma ya kamata Shugaban Kasa ya san halin da ake ciki,” a cewar Ortom.

Ba gudu ba ja da baya —CBN

Babban Bankin Najeriya CBN ya ce ba gudu ba ja da baya game da wa’adin da ya sanya na daina amfani da tsoffin takardun kudin kasar –N200, N500, da N1000 – daga ranar 31 ga watan Janairu.

Gwamnan Babban Bankin, Godwin Emefiele ne ya bayyana haka bayan ganawar Kwamitin Babban Bankin kan tsare-tsaren kudi a ranar Talata.

Mista Emefiele ya jaddada cewa babban bankin ya bayar da wadataccen lokaci ga ’yan kasar da su mayar da tsoffin kudadensu zuwa bankunan kasar domin musanya su da sabbi.

Tuesday, 24 January 2023

Babu Gudu Ba Ja Da Baya Kan Wa’adin Tsofaffin Kudade – Emefiele

Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Godwin Emefiele, ya ce babu gudu babu ja da baya kan wa’adin daina karbar tsofaffin takardun kudade a ranar 31 ga watan da muke ciki.

Emefiele ya jaddada kudurin babban bankin na daina amfani da kudade a ranar Talata a Abuja.

Mun lalata miyagun kwayoyi na N95bn a Kwatano – NAFDAC
‘An kashe ’yan sa-kai 1,773 a rikicin Boko Haram a Arewa maso Gabas’
Ya ce “Ba ni da wani sabon labari ga wadanda suke so a tsawaita kwanakin daina karbar tsofaffin takardun kudade.

“Mutane sun tara kudade a gidajensu kuma suna sane da cewar ba su da lasisin yin hakan.”


Ya ce CBN ya samu nasarar karbar sama da tiriliyan 1.5, kuma yana sa ran cimma tiriliyan 2 kafin wa’adin ya cika a karshen watan nan.

Ya ce “Mun roki Hukumar Yaki Da Masu Yi Wa Tattalin Arziki Zangon Kasa (EFCC) da Hukumar Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa (ICPC) da kada su musgunawa kowa kan mika tsofaffin kudaden bankuna, kuma saboda ni sun tabbatar da min ba za su yi komai ba,” in ji shi.

Wannan dai na zuwa ne bayan da jama’a da dama ke korafin cewar wa’adin da CBN ya bayar na daina amfani da tsofaffin kudaden ya yi kadan, inda mutane suke tsimayin a kara wa’adin.
(AMINIYA) 


Monday, 23 January 2023

Kotu Ta Bayar Da Umarnin Gurfanar Da Tukur Mamu

Wata Babbar Kotu a Jihar Kaduna, ta bayar da umarnin gurfanar mawallafin Jaridar Desert Herald, Alhaji Tukur Mamu a gaban kuliya.

Kotu ta nemi Hukumar Tsaro ta Farin Kaya reshen Jihar Kaduna (SSS) da kuma Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya, Abubakar Malami da su gaggauta gurfanar da Mamun ne tare da wasu mutum biyar.

Everton ta kori Frank Lampard
An tsaurara matakan tsaro a Legas gabanin ziyarar Buhari
Bayanai sun ce ababen zargin da kotun ta nemi a gurfanar da su bisa ga madogara ta binciken da aka yi a kansu sun hada; Tukur Mamu, Faisal Tukur Mamu, Ibrahim Hussain Tinja, Abdullahi Mashi, Mubarak Hussain Tinja da Yahaya Bello.

Da yake zartas da hukunci kan karar mai dauke da kwanan watan 15 ga Disambar 2022, Alkakin Kotun Mai Shari’a E. Andow, ya ce Kundin Tsarin Mulkin Najeriya ya yi tanadin bai wa duk wani wanda ake zargi ’yancin gurfanar da shi a gaban kuliya hadi da tuhume-tuhume da masu kara za su gabatar.


Umarnin kotun na zuwa ne watanni bayan da jami’an tsaron kasa da kasa na Interpol suka cafke tsohon mai shiga tsakanin gwamnati da ’yan ta’adda a kokarin kubutar da fasinjojin jirgin kasan nan na Abuja zuwa Kaduna da aka sace a watan Maris na bara.

A watan Satumbar bara ne aka kama Mamu a birnin Alkahira na kasar Masar yayin da yake jiran jirgi domin tafiya kasar Saudiyya inda zai gabatar da aikin Umrah

Mutane biliyan biyar ka iya kamuwa da bugun zuciya a duniya


Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta ce, kimanin mutane biliyan biyar na fuskantar gagarumin hatsarin kamuwa da ciwon zuciya saboda cin abinci mai dauke da kitse da ta bayyana amatsayin gubaL

A shekarar 2018 ne, Hukumar Lafiyar ta Duniya ta yi roko da a kawar da cimakar da ke dauke da kitse ganin yadda mutane dubu 500 suka yi mutuwar-farar-daya a sassan duniya sakamakon wannan cimakar.

WHO ta ce, kasashen duniya 43 da ke dauke da jumullar mutane biliyan 2 da miliyan 800, sun dauki matakin daina kalace da irin wannan cimakar a kasashensu, amma har yanzu akwai mutanen duniya kimanin biliyan biyar da aka gaza ba su kariya a sassan duniya.

WHO ta ce, Masar da Australia da Koriya ta Kudu, na  cikin kasashen duniya da suka yi watsi da gargadinta duk da cewa, su ke kan gaba a jerin kasashen da aka fi samun masu kamuwa da ciwon zuciya skamakon yawan cin abinci mai kitse.

Ana yawan cakuda wannan kitsen a cikin cimaka daban-daban da suka hada da man girki da abincin gwangwani da wasu kunsassun kayan kwalama.

Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya, Tedros Adhanom Ghebreyesus ya ce, irin wannan kitsen na dauke da sinadarin guba mai kisa , kuma ya kamata a daina amfani da shi a abinci.

Kamfanoni dai na sanya kitsen ne da zummar hana abinci lalacewa da wuri, sannan yana da saukin samu fiye da sauran sinadarai masu kara wa abinci tsawon wa’adin lalacewa.

(RFI)

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

Gimba Kakanda Celebrates Abdulmumin Jibrin at 50

Public affairs commentator and writer, Gimba Kakanda, has described Hon. Abdulmumin Jibrin as an archetype of a young Nigerian w...