Farashin kayan abinci, man fetur da takin zamani ya ƙaru saboda yaƙin Gabas ta Tsakiya: MDD

Hukumar Abinci da Noma ta Majalisar Dinkin Duniya (FAO) ta ce Ƙididdigar Farashin Abinci, wadda ke bayar da bayanai kan sauye-sauyen farashin abinci a kowane wata a farashin ƙasa da ƙasa, ta nuna an samu ƙaruwa da kashi 2.4 cikin 100 a watan Maris.


Wannan shi ne karo na biyu a jere na tashin farashin, kuma hukumar ta ce babban dalilin shi ne ƙarin farashin makamashi / Reuters
3 Afrilu 2026

Yaki tsakanin Isra'ila da Amurka kan Iran da martanin Tehran sun jawo ɗagawar farashin kayan abinci biyo bayan ƙarin farashin makamashi da taki, in ji hukumar abinci ta Majalisar Dinkin Duniya a ranar Juma'a.

Hukumar Abinci da Noma ta Majalisar Dinkin Duniya (FAO) ta ce Ƙididdigar Farashin Abinci, wadda ke bayar da bayanai kan sauye-sauyen farashin abinci a kowane wata a farashin ƙasa da ƙasa, ta nuna an samu ƙaruwa da kashi 2.4 cikin 100 a watan Maris idan aka kwatanta da Fabrairu.

Wannan shi ne karo na biyu a jere na tashin farashin, kuma hukumar ta ce babban dalilin shi ne ƙarin farashin makamashi da ke da alaƙa da rikici a Gabas ta Tsakiya.

A cikin ƙididdigar, rukunin man gyaɗa shi ne farashinsa ya fi ɗagawa inda shi ne mafi tsananin tashin farashi, wato kashi 5.1 cikin ɗari fiye da Fabrairu, yayin da farashin man ja ya kai matakin da bai taɓa kaiwa ba tun tsakiyar 2022, sakamakon tasirin tashin farashin mai ɗanyen man fetur, in ji FAO.

Duk da haka, rashin yankewar samar da hatsi ya rage illar wannan tashin farashin, in ji FAO.

(TRT Africa)

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki