Search This Blog

Monday, 1 May 2023

Duk da tsadar aikin Hajjin bana, kujeru 3,132 na Bauchi sun ƙare har ana nema

 


Kujerun aikin hajji 3,132 da Hukumar Alhazai ta
Ƙasa, NAHCON ta baiwa jihar Bauchi sun ƙare ƙarƙaf, duk da tsadar kudin aikin hajjin na bana da ya kai N2,919,000.

Babban Sakataren Hukumar Alhazai ta Bauchi, Imam Abdurrahman Ibrahim Idris ne ya bayyana haka a wani shiri na addini da rayuwa na gidan talabijin na NTA Bauchi, wanda ya gudana jiya Asabar 29 ga Afrilu, 2023.

A wata sanarwa da Muhammad Sani Yunusa Jami’in Yada Labarai na hukumar ya fitar a yau Lahadi, ya ce shirin talbijin din wani yunkuri ne na hukumar don sanar da al’umma halin da ake ciki kan shirye-shiryen aikin Hajjin 2023.

Imam Abdurrahman ya ce “Ba mu da sauran gurbi na kujerun aikin hajji, amma mun mika bukatar ga hukumar alhazai ta kasa don neman kari wa maniyyatan mu”.

Ya alakanta tashin farashin hajjin bana da tsadar masaukai a kasar Saudiyya da kuma faduwar darajar Naira akan Dalar Amurka.

Da ya taɓo batun bita, Imam Abdurrahman ya ce ba a yin ibada cikin jahilci, inda ya kara da cewa neman ilimi ga musulmi don bashi damar gudanar da ayyukansa na ibada yadda ya kamata ya zama tilas.              

Ya roki malaman bita a cibiyoyin bita da ke fadin jihar da su tallafawa maniyyata yadda ya kamata, inda ya kuma ja hankalin maniyyatan da su yi anfani da damarsu don sanin hukunce+hukuncen aikin Hajji.

Ya yi amfani da kafar sadarwar wajen nanata kudurin Gwamna Bala Abdulkadir Muhammad na ganin jihar Bauchi ta ci gaba da rike sunanta a matsayin Wanda tayi fice wajen tallafawa alhazai.

DN

Sunday, 30 April 2023

Gyara a dokar aikin Hajji zai rage tsadar tafiya Makkah a Najeriya - Sanata Dan Baba

Dan Majalisar Dattijai mai wakiltar Sokoto ta Kudu a Majalisar Dokokin Najeriya Sanata Ibrahim Abdullahi Dan Baba ya sha alwashin yin duk abin da zai iya wajen ganin an yi wa dokar aikin Hajji kwaskwarima a sabuwar majalisa ta goma da za ta fara aiki.

Sanatan wanda ya kasance a tsohuwar majalisa ta tara wacce za ta gama aikinta cikin watan Mayun shekaran nan ta 2023 ya ce tun da farko ya gabatar da kudurin gyaran a gaban majalisar mai karewa.

Sanata Dan Baba ya kara da cewa lokaci ya yi da ya kamata a samar wa mahajjata sauki wajen biyan makudan kudade domin aikin Hajji.

A cewar dan majalisar, yin gyara ga dokar Hukumar Aikin Hajji ta kasar shi ne zai magance yadda ake samun karuwar kudin tafiya Hajjin.

 Ya ce ya bukaci majalisa ta gudanar da bincike kan badakalar da ke cikin aikin Hajji a Najeriya kuma majalisar ta kafa wani kwamitin bincike.

"Biciken ya gano ana sama da fadi da kudaden mahajjata, otel da ya kamata a kama na kwana arba'in sai a kama na tsawon kwana casa'in sauran kwanakin kuma sai a sanya Larabawa a dakunan bayan alhazai sun tafi, sai a raba kudin tsakanin masu otel da kuma shugaban Hukumar Alhazai na wancan lokacin inda otel zai dauki kashi 25 shi kuma shugaba ya dauki kashi 75" A cewar Sanata Baba. 

Saudiyya ta bai wa Najeriya kujeru 95,000 a Hajjin 2023
21 Disamba 2022
Mene ne bambancin yin Umrah cikin azumi da sauran lokuta?
16 Aprilu 2023
Ana nuna mana bambanci a Saudiyya – Alhazan Najeriya
11 Yuli 2022
Dan majalisar ya ce kadan daga cikin kudaden da aka gano an wawure sun kai Naira biliyan daya.

Sanatan ya kara nuna bukatar yin kwaskwarima ga dokar wadda za ta hana duk wanda zai shugabanci hukumar ya yi abin da aka yi a baya.

Dan majalisar yana ganin Naira miliyan uku sun yi tsada ga masu zuwa aikin Hajji kuma da an dauki matakan da suka dace da kudin aikin Hajjin bai kai haka tsada ba a cewarsa.

Ya kuma kara da cewa lallai sai ya sake tayar da maganar a sabuwar majalisa har sai an bai wa mahajjata hakkinsu.

An shafe shekaru da dama ana kwan-gaba-kwan-baya kan batun yin gyara ga dokar a gaban majalisar dokokin ta Najeriya.
BBC 

APC Group Calls For All Stakeholders To Consider Senator Barau As Next Senate President

Kano Chapter of APC national supporters center calls for all stakeholders to consider senator Barau Jibirin as the next Senate president of the 10th Senate.

In a statement signed by its State Coordinator, Aliyu A Aliyu, the Group argued that his widespread acceptance, pragmatic leadership skills have made him the best to be considered as the next Senate president.

Accordingly his perfection to duty especially as Chairman Senate committee on appropriation defined his competency.

North West support for APC especially Kano that produced about two million votes in 2015,over a million votes in 2019 and five hundred and thirteen thousand votes this year need to be considered by the party's leadership in the incoming administration of Bola Ahmed Tinubu.

The Group advice APC and the president elect not to neglect Kano by doing so it can jeopardize the party chances in the future.

It called on senators to support Barau Jibirin in his effort to bring about purposeful leadership.

Under the current administration of President Buhari Lagos alone got vice president, speaker House of Representatives and National leader of the party.

Accordingly the Group will organize a peaceful two million man march in support of Barau Jibirin in Kano state as he is the only Candidate that win thirteen local Governments of his senatorial zone.

Democracy is the Government of the people by the people to the people.


Wutar Lantarki: Katse Layin KEDCO A Kano Somin-Tabi Ne —TCN

Kamfanin Samar da Wutar Lantarki na Kasa (TCN) ya ce katse wutar da ya yi wa Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na KEDCO a Jihar Kano somin-tabi ne.

Wasu sassan Jihar Kano sun yi kwanaki a cikin duhu bayan TCN ya katse layin wutar da suke kai saboda taurin bashin da yake bin KEDCO.

TCN ya katse wasu layikan wutar KEDCO mai kula da jihohin Kano da Jigawa da Katsina bayan kokarinsa na ganin kamfanin ya biya bashin ya faskara.

Mataimakin Janar-Manajan TCN na Shiyyar Kano, Bello Muhammad da kuma kakakin KEDCO, Sani Bala Sani, sun tabbatar cewa TCN ya katse wutar a ranar 26 ga watan Afrilu da muke ciki.


Layukan wutar da TCN ya kashe a Kano su ne Club Road da CBN da kuma Flour Mills (Dan Agundi), wanda hakan ya jefa yankunan da ke samun wuta daga nan a cikin duhu na tsawon kwanaki.

Tun ranar 24 ga watan ranar 24 ga wata Babban Jami’in Kasuwanci na TCN, E. A. Eje ya sanar cewa, “TCN ya ba da umarnin katse wutar KEDCO saboda saba ka’idar biyan bashi.”

Ya bayyana cewa katse layikan somin-tabi ne kafin TCN ya katse wutar gaba daya idan kamfanin bai biya bashin ba.

Ya bayyana cewa katse layikan somin-tabi ne kafin TCN ya katse wutar gaba daya idan kamfanin bai biya bashin ba.


Ya ce, “Mun riga an sanar da KEDCO da duk wadanda ake bi bashi game da saba alkawarin nasu; Mun kuma wallafa a jarida inda muka bayyana ranar da za mu yanke musu wuta bisa tsarin kasuwancin, kuma har wa’adin ya wuce.”


Amma mai magana da yawun KEDCO, Sani Bala Sani, ya ce, “Duk da haka, kamfanin na aiki tare da TCN da sauran masu ruwa da tsaki domin ganin an daidaita nan ba da jimawa ba.”

Sani ya ba wa jama’a hakuri, da alkawarin tabbatar da sama musu wutar lantarki mai inganci.
AMINIYA 

Saturday, 29 April 2023

Gwamnatin Tinubu Ce Za Gudanar Da Kidaya —Buhari

 


Shugaba Muhammadu Buhari ya amince a dage lokacin gudanar da Kidayar Jama’a da Gidaje da aka shirya farawa ranar 3 ga watan Mayu mai kamawa.

Kwana hudu kafin fara aikin Buhari ya ce ya bai wa gwamnati mai jiran gado damar yanke shawara kan lokacin gudanar da kidayar domin tabbatar da nasararsa.

Ya sake dage lokacin gudanar da kidayar ne bayan wata ganawa da tsakanin Shugaba Buhari da shugaban hukumar, Nasir Isa Kwarra tare da Majalisar Zartarwa ta Tarayya a ranar Juma’a a Fadar Shugaban Kasa.

Sanarwar da Ministan Yada Labarai da Raya Al’adu, Lai Mohammed ya fitar ta ce duk da haka Shugaba Buhari ya jaddada muhimmancin gudanar da kidayar wadda rabon da a gudanar shekara 17 ke nan.

Shugaban ya kuma yaba da kyakkyawatan shirin da hukumar ta yi wa kidayar, wanda zai tabbatar da ingancinsa kamar na sauran kasashen duniya.

Wata majiya a hukumar ta ce an dage aikin kidayar ne saboda wasu matsalolin da hukumar ke fuskanta da za su hana ta gudanar da aikin a lokaci guda; sai dai ba ta yi karin bayani ba.

Idan za a tuna, Hukumar Kidaya ta Kasa ta dage aikin daga 27 ga watan Maris zuwa ranar 3 ga watan Mayu, saboda kauce wa cin karo da zaben gwamnoni da aka kara wa lokaci.

A baya-bayan nan hukumar ta dakatar da horar da ma’aikatan wucin-gadi da za su gudanar da aikin, saboda matsalolin kudi da na jigila da sauransu.

A ranar Alhamis shugaban hukumar kidayar, Nasir Isa Kwarra ya shaida wa wakilan kasashen waje a Abuja cewa ba duka na’urorin aikin da hukumar take bukata ne suka shiga hannunta ba.

Amma ya ce nan gaba kadan hukumar za ta karbi cikon na’urori 300,000 da suka rage daga cikin na’urori 800,000 da za a yi amfani da su.

Duk bayan duk shekara 10 ake gudanar da kidaya Najeriya, amma yanzu shekara 17 tun tun bayan wanda kasar ta gudanar a shekarar 2006.

AMINIYA

’Yan Bindiga Sun Sako 70 Daga Cikin Yara 85 Da Suka Sace A Zamfara

 


’Yan ta’adda da suka yi garkuwa da yara sama da 85 a Jihar Zamfara sun sako 70 daga cikin yaran, amma sun kashe biyu.

A ranar Juma’a ’yan ta’addan suka sako yaran, kimanin mako uku bayan sun sace su daga kauyen Wanzamai na Karamar Hukumar Tsafe ta jihar.

Wani mazaunin yankin Sani Aliyu ya ce, “Yara biyu da ’yan bindigar suka kashe sun yi kokarin tserewa ne, wadanda aka sako din kuma sun galabaita saboda tsananin yunwa, kuma yanzu ana duba lafiyarsu.”

Ya ce ganin irin galabaitan da yaran suka yi ya sa iyayensu koke-koke, kuma “An sako su ne bayan an biya kudin fansa Naira miliyan shida; da farko miliyan uku aka ba su, amma suka ki sako su, sai an kara musu da sabbin babura guda biyu.”

Wakilinmu ya yi kokarin jin ta bangaren Rundunar ’Yan Sandan Jihar Zamfara, amma hakarsa ta yin magana da kakakin rundunar, CSP Muhammad Shehu, ba ta cim ma ruwa ba.

Kimanin makonni uku da suka gabata ne ’yan bindiga suka  ritsa wasu yara da suka je neman icen girki da wasu manya a gonaki suka yi awon gaba da su a yankin Tsafe na Jihar Zamfara.

Daga cikin manyan da ’yan bindigar suka yi garkuwa da su har da mata.

AMINIYA

Ba Ma Yi Wa Shirin Mika Mulki Zagon Kasa - Ganduje

Gwamnatin jihar Kano  ta ce a shirye take domin miƙa mulki ga sabuwar gwamnati cikin ruwan sanyi ba tare da tayar da ƙura ba.

Cikin wata sanarwa da ta fitar mai ɗauke da sa hannun kwamishinan yaɗa labarai Muhammad Garba, gwamnatin ta ce tuni aka samar da babban kwamiti da kuma ƙanana da za su taimaka domin ganin an miƙa mulkin salin alin.

Ya musanta iƙirarin jam’iyyar NNPP da ta ke jiran karɓar mulki na cewa gwamnatin Ganduje na yi wa shirin miƙa mulki zagon ƙasa.

Kwamishinan ya ƙara da cewa kwamitin miƙa mulki na ɓangaren gwamnatin Ganduje na rubuta rahoton ƙarshe kafin miƙa mulki. Ya bayyana cewa kamata ya yi kwamitin karɓa na gwamnati mai jiran gado shi ma ya shirya domin karɓar rahoton, wanda ya yi alƙawarin miƙawa a kan lokaci.

Muhammad Garba ya ƙara da cewa manufar miƙa mulki shi ne gwamnati mai sauka ta miƙa duk wasu abubuwa na tafiyar da shugabanci cikin ruwan sanyi. Ba yunkurin yaɗa wani tunani ko wata aƙida ba.

Ya kuma ce kamata ya yi gwamnati mai jiran gado ta mayar da hankali game da shirin da take yi na karɓar mulki, ta kuma kiyaye duk wani abu da zai iya janyo fitina a yayin miƙawar.

Ƙorafin da NNPP ta yi a jiya shi ne gwamnatin ta ba ta gurbi uku kawai a cikin kwamitin da aka kafa don miƙa mulki hannun sabuwar gwamnati.

BBC 

Labari da dumiduminsa : Shugaba Buhari Ya Dage Kidayar 2023

A wata ganawa da ya yi da mambobin majalisar zartaswa ta tarayya da kuma shugaban hukumar kidaya ta kasa, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da dage kidayar yawan jama’a da gidaje na shekarar 2023, wadda aka shirya gudanarwa tun daga ranar 3-7 ga watan Mayun 2023. Za a tantance sabon ranar ne ta hanyar gwamnati mai shigowa.


An cimma matsayar ne bayan taron ya jaddada muhimmancin da ke akwai na kidayar jama’a, wanda ba a yi ta tsawon shekaru 17 ba, na tattara sabbin bayanai domin inganta rayuwar ‘yan Nijeriya, da kuma fitar da manufofin ci gaban kasar. Duk da irin gagarumin ci gaban da aka samu da suka hada da kammala aikin tantance yankin da kuma daukar ma'aikata da horar da ma'aikata, shugaban ya bayyana cewa kamata ya yi gwamnati mai jiran gado ta samu damar karfafa wadannan nasarori.

Shugaba Buhari ya yaba wa tsarin hukumar kidaya ta kasa, musamman yadda ake tura na’urorin zamani domin tabbatar da kidayar jama’a mai inganci kuma abin dogaro. An umurci hukumar da ta ci gaba da shirye-shiryen kidayar jama’a don dorewar nasarorin da aka samu.

Taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati da suka hada da babban lauyan gwamnatin tarayya kuma ministan shari’a, Abubakar Malami; ministar kudi, kasafi da tsare-tsare ta kasa, Mrs Zainab Ahmed; ministan yada labarai da al'adu, Alhaji Lai Mohammed; Karamin Ministan Kasafi da Tsare-Tsare na Kasa, Mista Clem Agba da Sakataren Gwamnatin Tarayya, Mista Boss Mustapha.


A wata sanarwa da ministan yada labarai da al’adu, Alhaji Lai Mohammed ya fitar a ranar 29 ga Afrilu, 2023, an sanar da jama’a shawarar dage kidayar.
NIGERIAN TRACKER 

Friday, 28 April 2023

PDP Ta Bukaci Sanyawa Buhari Takunkumi

Babbar jam’iyyar adawar Najeriya ta PDP ta bukaci kasashen duniya da su hana shugaban kasa Muhammadu Buhari bizar tafiye tafiye da zaran ya mika mulki ranar 29 ga watan gobe, saboda abinda ta kira kalamansa dangane da zaben shugaban kasar da akayi ranar 25 ga watan Fabarairu. 


Yayin tsokaci akan zaben, Buhari ya bayyana ‘yan adawar Najeriya a matsayin wadanda suka shantake akan cewar zasu samu nasara ba tare da neman goyan bayan jama’a kamar yadda jam’iyarsa ta APC tayi ba. 

Sakataren hulda da jama’a na jam’iyyar Debo Ologunagba yace kalaman shugaban na iya tinzira jama’a da kuma haifar da illa ga zaman lafiyar kasar. 

Ologunagba ya kuma ce kalaman na iya karfafawa alkalai gwuiwa wajen yanke hukunci akan karar da suka shigar a gaban kotu domin kalubalantar sakamakon zaben wanda yace tuni wasu a ciki da wajen kasar ke bayyana shi a matsayin mafi muni a tarihin Najeriya. 

Jam’iyyar PDP tace zaben da akayi bana ya gamu da matsalolin da suka sabawa kundin tsarin mulkin kasa da kuma dokar zabe ta shekarar 1999 da kuma 2022 musamman abinda ya shafi wallafa sakamako daga tashoshin zabe da kuma aikewa da su kai tsaye zuwa cibiyar hukumar ta kasa. 

Kakakin jam’iyyar ya jaddada cewar suna da yakinin cewar basu fadi zabe ba, kamar yadda shugaba Buhari ke fadi, kuma ba zasu bada kai bori ya hau ba duk da barazanar da gwamnatin APC ke musu. 

Jam’iyyar tace ganin yadda Buhari ya yiwa dimokiradiya illa a Najeriya, suna bukatar kasashen duniya da su kakaba masa takunkumi da kuma hana shi da iyalansa tafiye tafiye da zaran ya mika mulki ranar 29 ga wata. 

Ologunagba yace wannan bukatar tasu tayi dai dai da bukatar da shugaba Buhari ya gabatarwa kungiyar kasashen Turai a ranar 17 ga watan Fabarairun shekarar 2022 lokacin da ya ziyarci kungiyar EU a Brussels. 

RFI

Ci-da-zucin 'yan adawa ne ya kayar da su zaɓe - Buhari

Shugaba Muhammadu Buhari ya ce ya yi imani ci-da-zuci ne babban abin da ya janyo taron 'yan adawar Najeriya suka sha kaye a zaɓen shugaban ƙasa da ya wuce.

Ya bayyana haka lokacin da ya karɓi gwamnonin jam'iyyarsa ta APC a ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abubakar Atiku Bagudu na jihar Kebbi.

Yana cewa a daidai lokacin da jam'iyya mai mulki take aiki tuƙuru don ci gaba da mulki a zaɓukan da aka yi a baya-bayan nan, 'yan adawa suna can sun cika da ci-da-zuci.

"Sun je suna ta faɗa wa masu goya musu baya a ƙasashen waje cewa, sai sun kayar da APC.

Yayin zaɓen na 25 ga watan Fabrairu, ɗan takarar jam'iyyar APC mai mulki Bola Ahmed Tinubu ya smau ƙuri'a 8,794,726.

Sai Atiku Abubakar, tsohon mataimakin shugaban ƙasar da ya samu ƙuri'a miliyan 6,984,520.

Ɗan takarar jam'iyyar Labour, Peter Obi yana da ƙuri'a miliyan 6,101,533, yayin da tsohon gwamnan Kano, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya zo na hudu da ƙuri'a miliyan 1,496,687.


Shugaba Buhari ya ce jam'iyyarsu ta yi nasara ne saboda ta haɗa ƙwarin gwiwar da take shi da taka-tsantsan kuma ta yi aiki tuƙuru har ya kai ta ga nasara.

Ya ce yanzu ma ga shi ci-da-zucin yana haifar wa 'yan adawan ƙarin matsaloli fiye da kowa.

"Abin na yi musu wahala su yi wa masu goyon bayansu na ƙasashen waje gamsasshen bayani a kan abin da ya sa suka gaza kayar da mu," in ji Buhari.

A cewarsa, sun haɗa ci-da-zuci da ji-ji-da-kai da bahagon lissafi, kuma su ne suka ja musu faɗuwa a zaɓukan bana. "Wannan ya sake haifar da ƙarin matsaloli a cikinsu. ta kai har ana tambaya. Me ya sa suka kasa kayar da mu?"

Shugaba Buhari ya ce babban dalilin da ya sa shi taya Asiwaju Bola Ahmed Tinubu murna kan nasarar da ya samu, shi ne 'yan adawa sun samu goyon baya, kuma masu goyo musu bayan daga ƙasashen waje sun lasa musu zuma a baki.

"Hakan ta sa sun tafi da burin cewa za su ci zaɓe, za su kayar da mu.

Wanne irin kuskure ne wannan?" shugaban ya sake tambaya.

'Kaduna zan koma bayan na huta a Daura'
Shugaba Buhari ya kuma yi bayani game da burinsa na rayuwa bayan sauka daga mulki, inda ya ce ya yi niyyar komawa gidansa na Daura, inda zai zauna tsawon wata shida kafin ya koma Kaduna.

Sanarwar Mallam Garba Shehu mai magana da yawun shugaban ƙasar, ta ambato Buhari yana yaba wa "Gwamna Nasir El-Rufa'i na Kaduna saboda ƙoƙarin da ya yi wajen samar da ababen more rayuwa da za su kyautata rayuwarsa da ta al'ummar jihar bayan ya kammala mulki".


Tun bayan sanar da sakamakon zaɓen 25 ga watan Fabrairu, masu sharhi kan al'amuran siyasa a Najeriya, suka yi ta tsokaci game da sakamakonsa.

Idan da 'yan adawan ƙasar sun haɗa ƙarfi wuri ɗaya, mai yiwuwa da cikin sauƙi, sun cinye zaɓen shugaban ƙasa.

Ana dai ɗora alhakin faɗuwar jam'iyyun adawar na Najeriya ne a kan matsalar rarrabuwar kai, da shiga zaɓe a lokacin da suke fama da ɓaraka.

'Yan takarar shugaban ƙasa a zaɓen watan Fabrairu guda biyu, Peter Obi da Rabi'u Musa Kwankwaso, duk sun ɓalle ne daga babbar jam'iyyar adawa ta PDP, wadda ta shiga zaɓen kuma tana fama da ɓaraka da rikicin cikin gida.

Idan an haɗa lissafin ƙuri'un da 'yan takarar biyu suka samu da na jagoran adawar Najeriya, Atiku Abubakar jimillar ƙuri'un za su kai 14,582,740.

Adadin dai ya kusa ninka abin da zaɓaɓɓen shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu ya samu, har suka ba shi nasara
 BBC 

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

SAPZ Kano partners ABCOAD to organize FFS Training for Youth and Women.

The Special Agro-Industrial Processing Zones (SAPZ) Programme, Kano State, in collaboration with Audu Bako College of Agricultur...