Search This Blog

Tuesday, 2 May 2023

Hajj2023 : Hukumar NAHCON Ta Sahalewa Kamfanin Max Air Yin Jigilar Alhazan Kano

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON, ta baiwa kamfanin Max Air damar jigilar maniyyatan jihar Kano 5,917 zuwa kasar Saudiyya a lokacin aikin Hajjin bana.

Idan ba a manta ba, matakin da NAHCON ta dauka na baiwa kamfanin Azman Air jigilar Alhazan jihar a shekarar da ta gabata ya fuskanci suka daga hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano da gwamnatin jihar.

A wata ganawa da manema labarai a ranar Talata, babban sakataren hukumar, Muhammad Abba Dambatta, ya bayyana cewa hukumar alhazan ta baiwa kamfanin Max Air aikin hajjin bana.

Ya kara da cewa kamfanin yana da inganci kuma yana da jiragen da za su iya jigilar alhazai sama da 1,000 a kowace rana.

Hakazalika, Dambatta ya kuma sanar da cewa hukumar ta rufe sabon rajistar aikin Hajji bisa umarnin NAHCON.

A cewarsa, Alhazan Jihar sun ci gajiyar kusan guraben aikin Hajji 6,000 da Hukumar Hajji ta ware musu, inda ya ce maniyyata 4,900 ne suka biya kudin Hajjin gaba daya, yayin da sauran wadanda suka ajiye Naira miliyan 2.5 za su biya sauran. daidaita cikin kwanaki biyu masu zuwa.

Sakataren zartarwa ya kuma bayyana cewa hukumar ta shirya tsaf domin gudanar da aikin Hajjin bana, yana mai cewa “Mun kammala dukkan shirye-shirye tun daga wurin kwana, ciyarwa, da jigilar kayayyaki daga Jeddah zuwa Makkah da Makkah zuwa Madina.

“Muna shirye don tashin jirgi. Mun yi tsari mai kyau wanda ya tabbatar da kudin da mahajjatan mu ke biya. Dambatta ya tabbatar da cewa mahajjatan mu za su ji dadin hidima a Saudiyya.
IHR

Monday, 1 May 2023

Labari cikin hotuna : Gwamna Ganduje Da Mataimakinsa Wajen Bikin Ranar Ma'aikata


Gwamnati Za Ta Cefanar Da Asibitin Fadar Shugaban Kasa

Gwamnatin Tarayya ta fara shirin cefanar da Asibitin Fadar Shugaban Kasa da wasu sassa da ke karkashin fadar gwamnatin ga ’yan kasuwa.

Babban Sakataren Fadar Shugaban Kasa, Tijjani Umar, ya ce Ma’aikatar Kudi da Kasa tare da Fadar Shugaban Kasar sun ware wasu ayyuka da tsare-tsare uku a Fadar Shugaban Kasa da gwamnati za ta fara yin hadaka da ’yan kasuwa wajen gudanar da su.

Wutar Lantarki: Minista ya ba da umarnin dawo da wutar Kano
’Yan bindiga sun kashe mutum 40 a Kebbi da Zamfara
Ya bayyana cewa Asibitin Fadar Shguaban Kasa da ke Abuja da Legas daya ne daga bangarorin da ake shirin shigo da ’yan kasuwa su zuba jari.

Sauran su ne Sashen Kula da Gandun Daji da kuma Dandalin Wasan Yara na Fadar Shugaban kasa.


’Yan Najeriya na yawan yin ce-ce-ku-ce game da yadda Shugaba Buhari ke zuwa duba lafiyarsa a kasashen waje.


A watannin baya dai Gwamnatin Tarayya ta yi kokarin yin dokar hana jami’an gwamnati zuwa duba lafiyarsu a kasashen waje, da nufin inganta yanayin bangaren lafiyar Najeriya.

Bangaren lafiyan Najeriya na fama da karancin likitoci, inda kwararrun likitoci ke tururuwar barin kasar domin yin aiki a kasashen waje.

Kungiyar likitoci ta Najeriya (NMA) ta bayyana cewa kasa da likitoci 15,000 ne suka rage a kasar mai yawan al’umma sama da miliyan 200.

A kan haka ne majalisar dokoki ta kasa take kokarin yin dokar da zai wajabta wa wadanda suka kammala karatu a fannin likita yin aiki aiki na shekara biyar a kasar kafin a ba su lasisi.
AMINIYA 


An Bawa Tsoho Dan Kasar Pakistan Da Ya Kwashe Shekaru 15 Yana Tara Kudin Aikin Umrah Kyautar Kujerar Hajji

Wani dattijo dan kasar Pakistan da ya fito a cikin wani faifan bidiyo a lokacin da yake fitowa daga Madina ya lashe zukatan miliyoyin al’ummar musulmin duniya saboda sanye da kaya mai sauki ba tare da takalmi a fuskarsu ba a lokacin da suke fitowa daga masallacin Annabi a watan Ramadan.

A wani al’amari da ba a saba gani ba, faifan bidiyon mutumin ya yadu a kafafen sada zumunta inda mutane ke nuna soyayyar su ga saukin kayan sa da kuma alaka da yanayin da ake gani a fuskarsa yayin da daya ke barin Masallatan Harami guda biyu.

An ce mutumin wanda ya fito daga Pakistan, makiyayi ne da ya tara isassun kudade sama da shekaru 15 don yin aikin Umrah.

Wannan shaharar da ya yi ba zato ba tsammani ta sa a yanzu ya samu kyautar Hajji da Umrah da dama daga Saudiyya da Pakistan da dama ciki har da abin da ma'aikatar nishadantarwa Turki Al Sheikh ya bayyana a Twitter.
IHR

Duk da tsadar aikin Hajjin bana, kujeru 3,132 na Bauchi sun ƙare har ana nema

 


Kujerun aikin hajji 3,132 da Hukumar Alhazai ta
Ƙasa, NAHCON ta baiwa jihar Bauchi sun ƙare ƙarƙaf, duk da tsadar kudin aikin hajjin na bana da ya kai N2,919,000.

Babban Sakataren Hukumar Alhazai ta Bauchi, Imam Abdurrahman Ibrahim Idris ne ya bayyana haka a wani shiri na addini da rayuwa na gidan talabijin na NTA Bauchi, wanda ya gudana jiya Asabar 29 ga Afrilu, 2023.

A wata sanarwa da Muhammad Sani Yunusa Jami’in Yada Labarai na hukumar ya fitar a yau Lahadi, ya ce shirin talbijin din wani yunkuri ne na hukumar don sanar da al’umma halin da ake ciki kan shirye-shiryen aikin Hajjin 2023.

Imam Abdurrahman ya ce “Ba mu da sauran gurbi na kujerun aikin hajji, amma mun mika bukatar ga hukumar alhazai ta kasa don neman kari wa maniyyatan mu”.

Ya alakanta tashin farashin hajjin bana da tsadar masaukai a kasar Saudiyya da kuma faduwar darajar Naira akan Dalar Amurka.

Da ya taɓo batun bita, Imam Abdurrahman ya ce ba a yin ibada cikin jahilci, inda ya kara da cewa neman ilimi ga musulmi don bashi damar gudanar da ayyukansa na ibada yadda ya kamata ya zama tilas.              

Ya roki malaman bita a cibiyoyin bita da ke fadin jihar da su tallafawa maniyyata yadda ya kamata, inda ya kuma ja hankalin maniyyatan da su yi anfani da damarsu don sanin hukunce+hukuncen aikin Hajji.

Ya yi amfani da kafar sadarwar wajen nanata kudurin Gwamna Bala Abdulkadir Muhammad na ganin jihar Bauchi ta ci gaba da rike sunanta a matsayin Wanda tayi fice wajen tallafawa alhazai.

DN

Sunday, 30 April 2023

Gyara a dokar aikin Hajji zai rage tsadar tafiya Makkah a Najeriya - Sanata Dan Baba

Dan Majalisar Dattijai mai wakiltar Sokoto ta Kudu a Majalisar Dokokin Najeriya Sanata Ibrahim Abdullahi Dan Baba ya sha alwashin yin duk abin da zai iya wajen ganin an yi wa dokar aikin Hajji kwaskwarima a sabuwar majalisa ta goma da za ta fara aiki.

Sanatan wanda ya kasance a tsohuwar majalisa ta tara wacce za ta gama aikinta cikin watan Mayun shekaran nan ta 2023 ya ce tun da farko ya gabatar da kudurin gyaran a gaban majalisar mai karewa.

Sanata Dan Baba ya kara da cewa lokaci ya yi da ya kamata a samar wa mahajjata sauki wajen biyan makudan kudade domin aikin Hajji.

A cewar dan majalisar, yin gyara ga dokar Hukumar Aikin Hajji ta kasar shi ne zai magance yadda ake samun karuwar kudin tafiya Hajjin.

 Ya ce ya bukaci majalisa ta gudanar da bincike kan badakalar da ke cikin aikin Hajji a Najeriya kuma majalisar ta kafa wani kwamitin bincike.

"Biciken ya gano ana sama da fadi da kudaden mahajjata, otel da ya kamata a kama na kwana arba'in sai a kama na tsawon kwana casa'in sauran kwanakin kuma sai a sanya Larabawa a dakunan bayan alhazai sun tafi, sai a raba kudin tsakanin masu otel da kuma shugaban Hukumar Alhazai na wancan lokacin inda otel zai dauki kashi 25 shi kuma shugaba ya dauki kashi 75" A cewar Sanata Baba. 

Saudiyya ta bai wa Najeriya kujeru 95,000 a Hajjin 2023
21 Disamba 2022
Mene ne bambancin yin Umrah cikin azumi da sauran lokuta?
16 Aprilu 2023
Ana nuna mana bambanci a Saudiyya – Alhazan Najeriya
11 Yuli 2022
Dan majalisar ya ce kadan daga cikin kudaden da aka gano an wawure sun kai Naira biliyan daya.

Sanatan ya kara nuna bukatar yin kwaskwarima ga dokar wadda za ta hana duk wanda zai shugabanci hukumar ya yi abin da aka yi a baya.

Dan majalisar yana ganin Naira miliyan uku sun yi tsada ga masu zuwa aikin Hajji kuma da an dauki matakan da suka dace da kudin aikin Hajjin bai kai haka tsada ba a cewarsa.

Ya kuma kara da cewa lallai sai ya sake tayar da maganar a sabuwar majalisa har sai an bai wa mahajjata hakkinsu.

An shafe shekaru da dama ana kwan-gaba-kwan-baya kan batun yin gyara ga dokar a gaban majalisar dokokin ta Najeriya.
BBC 

APC Group Calls For All Stakeholders To Consider Senator Barau As Next Senate President

Kano Chapter of APC national supporters center calls for all stakeholders to consider senator Barau Jibirin as the next Senate president of the 10th Senate.

In a statement signed by its State Coordinator, Aliyu A Aliyu, the Group argued that his widespread acceptance, pragmatic leadership skills have made him the best to be considered as the next Senate president.

Accordingly his perfection to duty especially as Chairman Senate committee on appropriation defined his competency.

North West support for APC especially Kano that produced about two million votes in 2015,over a million votes in 2019 and five hundred and thirteen thousand votes this year need to be considered by the party's leadership in the incoming administration of Bola Ahmed Tinubu.

The Group advice APC and the president elect not to neglect Kano by doing so it can jeopardize the party chances in the future.

It called on senators to support Barau Jibirin in his effort to bring about purposeful leadership.

Under the current administration of President Buhari Lagos alone got vice president, speaker House of Representatives and National leader of the party.

Accordingly the Group will organize a peaceful two million man march in support of Barau Jibirin in Kano state as he is the only Candidate that win thirteen local Governments of his senatorial zone.

Democracy is the Government of the people by the people to the people.


Wutar Lantarki: Katse Layin KEDCO A Kano Somin-Tabi Ne —TCN

Kamfanin Samar da Wutar Lantarki na Kasa (TCN) ya ce katse wutar da ya yi wa Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na KEDCO a Jihar Kano somin-tabi ne.

Wasu sassan Jihar Kano sun yi kwanaki a cikin duhu bayan TCN ya katse layin wutar da suke kai saboda taurin bashin da yake bin KEDCO.

TCN ya katse wasu layikan wutar KEDCO mai kula da jihohin Kano da Jigawa da Katsina bayan kokarinsa na ganin kamfanin ya biya bashin ya faskara.

Mataimakin Janar-Manajan TCN na Shiyyar Kano, Bello Muhammad da kuma kakakin KEDCO, Sani Bala Sani, sun tabbatar cewa TCN ya katse wutar a ranar 26 ga watan Afrilu da muke ciki.


Layukan wutar da TCN ya kashe a Kano su ne Club Road da CBN da kuma Flour Mills (Dan Agundi), wanda hakan ya jefa yankunan da ke samun wuta daga nan a cikin duhu na tsawon kwanaki.

Tun ranar 24 ga watan ranar 24 ga wata Babban Jami’in Kasuwanci na TCN, E. A. Eje ya sanar cewa, “TCN ya ba da umarnin katse wutar KEDCO saboda saba ka’idar biyan bashi.”

Ya bayyana cewa katse layikan somin-tabi ne kafin TCN ya katse wutar gaba daya idan kamfanin bai biya bashin ba.

Ya bayyana cewa katse layikan somin-tabi ne kafin TCN ya katse wutar gaba daya idan kamfanin bai biya bashin ba.


Ya ce, “Mun riga an sanar da KEDCO da duk wadanda ake bi bashi game da saba alkawarin nasu; Mun kuma wallafa a jarida inda muka bayyana ranar da za mu yanke musu wuta bisa tsarin kasuwancin, kuma har wa’adin ya wuce.”


Amma mai magana da yawun KEDCO, Sani Bala Sani, ya ce, “Duk da haka, kamfanin na aiki tare da TCN da sauran masu ruwa da tsaki domin ganin an daidaita nan ba da jimawa ba.”

Sani ya ba wa jama’a hakuri, da alkawarin tabbatar da sama musu wutar lantarki mai inganci.
AMINIYA 

Saturday, 29 April 2023

Gwamnatin Tinubu Ce Za Gudanar Da Kidaya —Buhari

 


Shugaba Muhammadu Buhari ya amince a dage lokacin gudanar da Kidayar Jama’a da Gidaje da aka shirya farawa ranar 3 ga watan Mayu mai kamawa.

Kwana hudu kafin fara aikin Buhari ya ce ya bai wa gwamnati mai jiran gado damar yanke shawara kan lokacin gudanar da kidayar domin tabbatar da nasararsa.

Ya sake dage lokacin gudanar da kidayar ne bayan wata ganawa da tsakanin Shugaba Buhari da shugaban hukumar, Nasir Isa Kwarra tare da Majalisar Zartarwa ta Tarayya a ranar Juma’a a Fadar Shugaban Kasa.

Sanarwar da Ministan Yada Labarai da Raya Al’adu, Lai Mohammed ya fitar ta ce duk da haka Shugaba Buhari ya jaddada muhimmancin gudanar da kidayar wadda rabon da a gudanar shekara 17 ke nan.

Shugaban ya kuma yaba da kyakkyawatan shirin da hukumar ta yi wa kidayar, wanda zai tabbatar da ingancinsa kamar na sauran kasashen duniya.

Wata majiya a hukumar ta ce an dage aikin kidayar ne saboda wasu matsalolin da hukumar ke fuskanta da za su hana ta gudanar da aikin a lokaci guda; sai dai ba ta yi karin bayani ba.

Idan za a tuna, Hukumar Kidaya ta Kasa ta dage aikin daga 27 ga watan Maris zuwa ranar 3 ga watan Mayu, saboda kauce wa cin karo da zaben gwamnoni da aka kara wa lokaci.

A baya-bayan nan hukumar ta dakatar da horar da ma’aikatan wucin-gadi da za su gudanar da aikin, saboda matsalolin kudi da na jigila da sauransu.

A ranar Alhamis shugaban hukumar kidayar, Nasir Isa Kwarra ya shaida wa wakilan kasashen waje a Abuja cewa ba duka na’urorin aikin da hukumar take bukata ne suka shiga hannunta ba.

Amma ya ce nan gaba kadan hukumar za ta karbi cikon na’urori 300,000 da suka rage daga cikin na’urori 800,000 da za a yi amfani da su.

Duk bayan duk shekara 10 ake gudanar da kidaya Najeriya, amma yanzu shekara 17 tun tun bayan wanda kasar ta gudanar a shekarar 2006.

AMINIYA

’Yan Bindiga Sun Sako 70 Daga Cikin Yara 85 Da Suka Sace A Zamfara

 


’Yan ta’adda da suka yi garkuwa da yara sama da 85 a Jihar Zamfara sun sako 70 daga cikin yaran, amma sun kashe biyu.

A ranar Juma’a ’yan ta’addan suka sako yaran, kimanin mako uku bayan sun sace su daga kauyen Wanzamai na Karamar Hukumar Tsafe ta jihar.

Wani mazaunin yankin Sani Aliyu ya ce, “Yara biyu da ’yan bindigar suka kashe sun yi kokarin tserewa ne, wadanda aka sako din kuma sun galabaita saboda tsananin yunwa, kuma yanzu ana duba lafiyarsu.”

Ya ce ganin irin galabaitan da yaran suka yi ya sa iyayensu koke-koke, kuma “An sako su ne bayan an biya kudin fansa Naira miliyan shida; da farko miliyan uku aka ba su, amma suka ki sako su, sai an kara musu da sabbin babura guda biyu.”

Wakilinmu ya yi kokarin jin ta bangaren Rundunar ’Yan Sandan Jihar Zamfara, amma hakarsa ta yin magana da kakakin rundunar, CSP Muhammad Shehu, ba ta cim ma ruwa ba.

Kimanin makonni uku da suka gabata ne ’yan bindiga suka  ritsa wasu yara da suka je neman icen girki da wasu manya a gonaki suka yi awon gaba da su a yankin Tsafe na Jihar Zamfara.

Daga cikin manyan da ’yan bindigar suka yi garkuwa da su har da mata.

AMINIYA