Search This Blog

Thursday, 19 January 2023

Jerin Kamfanonin da aka Amince don Samar Gidajen Makkah da masu samar da abinci a Aikin Hajji na 2023.


Labari Da Dumiduminsa: Jirgin farko na Aikin Hajin Bana Zai Fara Tashi Daga 21 ga Mayu zuwa karshen 22 ga Yuni - GACA

Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Saudiyya GACA ta fitar da jadawalin jigilar jigilar alhazai na ayyukan Hajji na 2023.

Wata sanarwa mai taken aikin Hajji da ke kula da jigilar alhazai da kamfanin jirgin na GACA ya fitar a yau ya nuna cewa filin jirgin zai bude jirgin farko mai dauke da alhazan 2023 a ranar Lahadi 21 ga watan Mayu 2023 kuma a rufe don masu zuwa aikin Hajji a ranar Alhamis 22 ga watan Yuni 2023.

A ranar Lahadi 2 ga watan Yulin 2023 ne za a fara jigilar Alhazai dauke da alhazan kasar Saudiyya na shekarar 2023, kuma za su kare a ranar Laraba 2 ga watan Agustan 2023.

Hukumar ta GACA ta kuma shawarci dukkan kasashen da ke halartar aikin hajji da su gabatar da bukatun aiki kafin karshen ranar aiki a ranar Litinin 29 ga watan Rajab kwatankwacin 20 ga Fabrairu 2023.

Sama da mahajjata miliyan 2 ne ake sa ran za su yi aikin hajjin shekarar 2023 a kasar Saudiyya

CBN zai hukunta wasu bankuna a Kano kan sabbin kuɗaɗe

 


Babban bankin Najeriya CBN ya ce zai dauki tsattsauran mataki kan wasu bankuna a Jihar Kano, saboda kin zuwa su karbi sabbin takardun naira da ya samar.

CBN reshen Jihar ta Kano ya jaddada matsayarsa kan cewa cewa karshen watan nan na Janairu zai daina karbar tsaffin kudaden kamar yadda ya sanar tun bara.

Al'umma a fadin Najeriya na ta kokawa kan karancin sabbin kudaden da CBN ya kaddamar a bankuna, baya ga korafin da suke yi na rashin bayar da cikakken wa'adi domin mayar da tsofaffin kudaden bankuna.

Shugaban CBN reshen Jihar Kano Malam Umar Ibrahim Biyu a tattaunawarsa da BBC ya ce, akwai isassun sabbin takardun kudaden bankuna kawai ake jira su je su karba.

"Mun yi magana da bankuna kan cewa su aiko mana da adadin kudin da suke bukata da za a zuba a na'urar ATM domin amfanin yau da gobe ga al'umma.

"Haka muka shaida musu, kuma tuni mun fara bayarwa. Sai dai korafe-korafe sun mana yawa kan ba a samun wadannan kudade a bankuna.

"Wannan dalili ne ya sa muka hau bincike domin tabbatar da cewa suna raba kudaden yadda muka cimma yarjejeniya da su, mun gano wadanda ba sa bayar da sabbin da muka basu," in ji Malam Umar Biyu.

A cewarsa wasu kuwa na hadawa sabbi da tsofaffi, amma binciken da suka fara gabatarwa ya sanya an samu gagarumin sauyi.

A yanzu idan kaje ATM za ka samu sababbin kudade a kusan ko ina a fadin Jihar Kano.

'Muna da isassun sababbin kudade amma ban san adadinsu ba'

CBN

ASALIN HOTON,CBN

A cewar shugaban bankin reshen jihar Kano tun bayan sanarwar da babban bankin ya fitar, suke bi kasuwanni domin wayar da kan 'yan kasa domin su gaggauta mayar da tsofaffin da suke da su a hannu ba tare da biyan kudade ba.

"Mun kara jaddada cewa babu wani dalili da zai sa a kara wa'adin da aka tsayar na daina karbar tsofaffin kudi a ranar 31 ga watan Janairun da muke ciki.

Wakilin BBC ya tambayi Malam Umar adadin kudaden da CBN ya aika musu reshen jihar Kano sai ya ce : "Babban bankin ya buga wadannan kudade isassu, ta yadda za su kai ko ina a kasar nan. Yana nan kuma yana ci gaba da bayarwa.

"A gaskiya ba zan iya fada maka adadin kudaden da aka aiko Kano ba da ka, amma an turo yadda ya kamata," in ji shugaban CBN na Kano.

Ya kara da cewa za su dauki mataki kan duk bankin da bai je ya karbi sabbin kudaden ba. 

A ranar Laraba 26 ga watan Oktoba ne Babban Bankin Najeriyar ya sanar da matakin sauya fasalin kudin kasar daga takardar naira 200 zuwa 1000, inda ya buƙaci masu kuɗi a hannu su mayar da su bankuna cikin ƙasa da kwana 50. 

Kazalika CBN din, ya ce sabbin kudaden da za a samar za su fara yawo a hannun mutane daga ranar 15 ga watan Disambar 2022, sannan kuma za a ci gaba da amfani da tsofaffin kudaden har nan da ranar 31 ga watan Janairun 2023.

(BBC HAUSA)

Akwai yiwuwar a soma cire tallafin fetur a watan Afrilu - Gwamnatin Najeriya

 


Akwai yiwuwar gwamnatin tarayyar Najeriya ta soma cire tallafin man fetur daga Afrilun 2023, wato watanni uku kafin yadda ainahin lokacin da aka yi niyyar cire tallafin a baya.

Ministar kuɗi da kasafi Zainab Ahmed ce ta bayyana haka a wata hira ta musamman da ta yi da gidan talabijin na Arise a yayin wani taro na tattalin arzikin duniya a Switzerland.

"Abin da ya fi shi ne wannan gwamnatin watakila ta soma cire tallafi a farkon zango na biyu na wannan shekara saboda zai fi nagarta idan aka cire a hankali a maimakon a jira a cire shi baki ɗaya," in ji ministar.

Ta bayyana cewa duka ƴan takarar shugaban ƙasar Najeriya a lokutan yaƙin neman zaɓensu duk suna da ra'ayin cire wannan tallafin

Bayan ƙara wa'adin watanni 18, gwamnatin tarayya ta shirya kashe naira tiriliyan 3.35 kan tallafin mai daga Janairu zuwa Yunin 2023.

Wannan ƙarin wa'adin da aka yi ya janyo muhawara matuƙa kan irin kuɗin da za a kashe sakamakon ana ganin cewa zai ƙara giɓi a kasafin kuɗi wanda kuma ana ganin idan aka samu giɓin sai an ranto kuɗaɗe.

Bankin duniya da Hukumar bayar da lamuni ta duniya IMF duk sun bayyana cewa cire tallafin man fetur na ɗaya daga cikin ginshiƙan da za su ɗaga Najeriya domin ta samu ci gaba.

An kusan shafe shekara guda ana cikin wahalar man fetur a Najeriya.

An soma wahalar fetur ɗin dai makonni kaɗan bayan an soma yaƙin Ukraine.

Dillalan man fetur dai a ƙasar a kullum na dora laifin kan gwamnati inda suke cewa suna bin basussuka kuma babu isashen mai.

Sakamakon wahalar man fetur ɗin ana sayar da man kan farashin da ya kai har 360 a wasu gidajen mai da ke faɗin ƙasar.

A kullum gwamnatin Najeriyar na cewa za ta kawo ƙarshen matsalar wahalar fetur ɗin amma abin ya ci tura.

(BBC HAUSA)

Wednesday, 18 January 2023

Duk Mai Son Mukami A Gwamnanatina Sai Ya Kawo Akwatinsa Lokacin Zabe - Atiku

Dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya ce duk dan jam’iyyar da ke neman kwagila ko mukami a gwamnatinsa, sai ya nuna sakamakon zaben mazabarsa kafin a ba shi.

Atiku ya bayyana hakan ne ranar Laraba a Abekuta babban birnin Jihar Ogun, yayin taron ganawa da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar.

Atiku ya ce halartar kowanne yakin neman zaben jam’iyyar ba shi ne tabbacin samun matsayi ko kwangila a gwamnatinsa ba, jajircewa wajen ganin an kawo akwatinan mazaba ne.

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar ya kuma ce, “Dukkanku magoya bayan PDP ne, kuma kuna so ta dawo mulki, don haka ina rokonku ku tabbatar kun kawo akwatinan mazabunku.

Yawon zuwa yakin neman zaben kafatanin ’yan takarar jam’iyya ba shi ne zai sa ka samu aiki ko matsayi ko kwangila ba idan an ci zabe, hanyar da kadai za ku samu shi ne nuna min sakamakon zaben mazabarku.

“Kuma ina bai wa kowanne dan takarar PDP umarnin yin hakan, domin da haka ne kadai za mu ci zabe.

Atiku ya kuma yi alkawarin farfado da bangaren ilimi da tattalin arziki, domin kawo karshen yajin aikin jami’o’i a Najeriya, da kuma inganta rayuwar ma’aikata da sauran al’umma.
(AMINIYA) 

Kotu A Kano Ta Daure Alkalai Kan Badakalar Kudin Marayu Naira Miliyan 99

Wata Kotun Majistare mai lamba 14 a Jihar Kano ta aike da wasu alkalai da ma’aikatan Hukumar Shari’a gidan gyaran hali saboda zarginsu da wawure Naira miliyan 99.

Aminiya ta ruwaito cewa Kotun, karkashin Mai Shari’a Mustapha Sa’ad Datti ta aike da mutanen ne bisa zargin su da yin sama da fadi da kudaden wadanda mallakin wasu marayu ne.

Tun da farko dai Hukumar Karbar Korafe-korafe da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano ce ta gurfanar da wasu alkalai da kuma ma’aikatan Hukumar Shari’ar Musulunci a gaban kotun.

Wadanda aka gurfanar a gaban kotun sun hada da Sani Ali da Sani Uba Ali da Bashir Baffa da Gazzali Wada da Hadi Tijjani Mu’azu da Alkasim Abdullahi da Yusuf Abdullahi da kuma Mustafah Bala.

Sauran sun hada da Jaafar Ahmad da Adamu Balarabe da Aminu Abdulhadi da Abdullahi Sulaiman Zango da Garba Yusuf da Bashir Ali Kurawa da kuma Usaina Imam.

Takardar karar ta bayyana cewa ana tuhumar alkalan da ma’aikatan shari’ar da laifin hada kai da cin amana da satar Naira miliyan 99, laifukan da dukkaninsu suka musanta.

Mai gabar da kara, Barista Zaharaddin Kofar Mata, ya roki kotun da ta ba su wata ranar domin sake gabatar da su a gaban kotun tare da kawo shaida.

Sai dai lauyoyin wadanda ake kara bakinsu ya zo daya a kan neman beli, kodayake kotun ta ki ta bayar da belin nasu, inda ta ce za ta bayyana matsayinta game da rokon belin a zamanta na gaba.

Daga nan ne sai alkalin ya dage sauraren shari’ar zuwa ranar daya ga watan Fabrairu, 2023.

Ma'aikatan BBC Hausa Da Dama, Sun Ajiye Aikinsu

Akalla ‘yan jarida tara na Sashen Hausa na BBC a Najeriya sun yi murabus a cikin wata daya da ya gabata a wani abin da aka bayyana da cewa ba a taba yin irinsa ba a tarihi 

Akalla ‘yan jarida tara na Sashen Hausa na BBC a Najeriya sun yi murabus a cikin wata daya da ya gabata a wani abin da aka bayyana a matsayin wanda ba a taba ganin irinsa ba a tarihin kafafen yada labarai na duniya.

Aminiya ta gano cewa ma’aikatan da abin ya shafa sun hada da manyan ‘yan jarida guda biyu, ’yan jarida uku na kafafen sada zumunta – biyu daga cikinsu manyan ‘yan jarida ne – babban mai ba da rahotannin harsuna biyu na Hausa/English Africa, mai ba da rahotannin kafafen yada labarai da kuma ‘yan jaridar bidiyo guda biyu.

An tattaro cewa yayin da biyar daga cikin ‘yan jaridar suka bar watan Disambar da ya gabata; Sauran hudun sun yi murabus ne a ranar Litinin din da ta gabata don shiga sabon sashen Afirka na Rediyo da Talabijin na Turkiyya (TRT) a Istanbul.

“Wannan lamari ba a taba ganin irinsa ba a tarihin BBC Hausa. Wasu ‘yan jarida tara na BBC Hausa sun shiga cikin shirin da za a fara aiki da shi nan ba da dadewa ba bayan da gwamnatin Turkiyya ta yanke shawarar kafa TRT Africa: Hausa, Swahili, French and English for Africa,” kamar yadda wata majiya ta BBC ta shaida wa wakilin Majiyarmu 

Majiyar ta ce Nasidi Adamu Yahaya, wanda ya yi murabus daga matsayin babban dan jarida na zamani, zai jagoranci sashen Hausa na TRT, tare da wata babbar ‘yar jarida mai suna Halima Umar Saleh a matsayin mataimakiyarsa.

Da aka tambayi daya daga cikin ‘yan jaridan da ya nemi a sakaya sunansa, da aka tambaye shi ko me ya kai ga yin murabus din da yawa, ya ce an dauki matakin ne kan yadda kafafen yada labarai na Turkiyya suka kuduri aniyar bayar da labarai masu kyau a Afirka.

Ya ce: “TRT tana son mu canza labarin ba da labari. Sauran kungiyoyin watsa labarai na kasa da kasa sun yi ta bayar da rahotanni musamman yunwa, yaƙe-yaƙe da sauran munanan labarai game da Afirka. Akwai kyawawan labarai masu kyau a Afirka - kasuwanci da damar yin aiki. Akwai dabi'un al'adu, wasanni, sabbin abubuwa; mutanen da ke da hannu a cikin aikin da ke da alaƙa da hankali. Wannan shine abinda Sashen Hausa na TRT zai kawo muku. Yawancin kafofin watsa labaru na duniya ba su ba da rahoton waɗannan abubuwa ba.

“Ba muna cewa ba za mu kai rahoton Boko Haram, ‘yan bindiga da sauran su ba, amma muna da wasu labarai masu kyau. Akwai labarun da suka shafi dan Adam akan Boko Haram. 

Muna son baiwa 'yan Afirka damarsu . Ya kamata a ji mutane game da labarunsu masu kyau; ba kawai labarai marasa kyau koyaushe ba.”
Dan jaridar, wanda kuma ya bayyana murabus din a matsayin "ba a taba yin irinsa ba," ya tabbatar da cewa "'yan jarida na karshe sun mika takardar murabus dinsu a ranar (Litinin)."

"Wasu daga cikinsu zasu bar aikin a ranar Litinin din nan, yayin da wasu za su tafi nan da 'yan kwanaki. Mu biyar muka tafi a watan Disamba. A Najeriya, BBC Hausa na da 'yan jarida sama da 40, amma yanzu kusan kashi daya bisa uku na mu za mu tafi. Bai taba faruwa a Sashen Hausa na BBC ba,” ya kara da cewa.

Kuskuren Shekara 24 Ne Ya Jefa Najeriya Halin Da Ta Ke Ciki — Kwankwaso

Dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce kuskuren da shugabannin baya suka yi a shekaru 24 da suka shude ne ya jefa Najeriya cikin tsaka mai wuyar da ta ke ciki a yanzu. 

Tsohon Gwamnan na Jihar Kano, ya bayyana haka ne a Landan yayin da yake amsa tambayoyi a ‘Chatnam House’ game zaben Najeriya na 2023.

’Yan takarar Gwamnan Kano sun rattaba hannu a kan yarjejeniyar zaman lafiya
Dattijuwar da ta fi kowa tsufa a duniya ta rasu tana da shekara 118
A cewarsa, “Za mu iya alakanta kowane irin abu da ake zargin su ne ke da alhakin halin da muke ciki, tun daga annobar Kwarona zuwa koma bayan tattalin arzikin duniya da sauransu.

“Amma a ni a ganina, mun fada halin da muke ciki ne saboda kuskuren da mutanen da aka dora wa alhakin mulkin Najeriya suka tafka a cikin shekaru 24 da suka gabata.”

Kwankwaso wanda kuma tsohon Ministan Tsaron Najeriya ne, ya lissafa manyan matsaloli da kasar nan ke ciki da suka hada da rashin tsaro, talauci, rashin aikin yi, hauhauwar farashin kayayyakin masarufi da kuma rashin isassun kayan aikin kiwon lafiya.

A cewarsa ragowar sun hada da rashin tsari mai kyau game da ilimi, cin hanci da rashawa, satar danyen mai da sauransu.

Kwankwaso ya ce ya shirya yin takarar shugaban kasa ne saboda ya gano wuraren da tsofaffin shugabannin kasar nan suka tafka kuskure, kuma ya ce jam’iyyarsa ta shirya gyara wadannan kurakuran.

“Mun shirya tsaf, kuma muna da tsarin da zai ciyar da Najeriya gaba tare sa warware kowace irin matsala da aka bari.”
(AMINIYA) 

LABARI CIKIN HOTUNA : Tawagar NAHCON A yayin Zaman tattaunawa da Kamfanin sanya Jari na KIDANA A Makka

Idan Mijina ya Gza bayan Shekara hudu, Ka da ku Sake Zabarsa - Matar Tinubu

 


Mai dakin dan takarar Shugaban Kasa na jamiyyar APC, Sanata Oluremi Tinubu, ta shawarci yan Najeriya da kada su sake zaben mijinta a karo na biyu idan ya gaza tabuka komai bayan shekara hudu.

Oluremi ta yi wannan kira ne a wajen gangamin yakin neman zaben Tinubu/Shettima na matan shiyyar Kudu maso Gabas wanda ya gudana a Owerri, babban birnin Jihar Imo.

Ta ce, “A ajiye batun addini a gefe, ni Kirista ce. Ko kun taba tunanin cewa wata rana za a samu ‘yan takara Kirista da Kirista?

“Me ya kamata ya zama madogara? Tun da mun jarraba ‘yan takara Musulmi da Kirista, bari mu jarraba wannan ma mu gani sannan bayan shekara hudu idan ba su tabuka komai ba kuna iya yin waje da su,” in ji ta.

Saboda a cewarta, “Idan ana da mutum mai tsoron Allah, ba wai Kirista ko Musulmi ba, amma dai mutum mai tsoron Allah. Idan mai tsoron Allah ya kasance rike da mulki zai ba ku kulawar da ta dace.

A matsayinta na wadda ta yi wa Najeriya hidima a matsayin matar Gwamna da kuma Sanata, Oluremi ta bai wa matan Najeriya tabbacin za su samu kaso mai tsoka muddin Tinubu/shettima suka kafa gwamnati.

“Yanzu lokacin yi wa Najeriya aiki ne. Ba wasa muke ba. Za mu tuna da mata kuma ina ba ku tabbacin cewa Asiwaju zai tuna da ku.

“Tinubu/Shettima na da kyakkyawan tanadi ga matasa. Za mu yi aiki da kowace shiyya a kan bukatunta,” in ji Oluremi.

Da yake tofa albarkacin bakinsa a wajen taron, Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma, ya yi kira ga matan shiyyar Kudu maso Gabas da su yi farar dabara sannan su zabi dan takarar shugabancin kasa na APC a zabe mai zuwa.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

Presidential delegation pays condolence visit to Hamza Darma’s family in Kano

A high-powered presidential delegation has paid a condolence visit to the family of late Alhaji Hamza Usman Darma, a prominent K...