Hukumar Kula da Yanayi ta Kasar Saudiyya ta ce, yanayin zafi a gobe Juma’a, zai kai daraja Hamsin na tsananin Zafi.

Saboda wannan zafin yanayin, Gwamnatin Saudiyya na bada shawarar cewa Alhazai da suyi Sallar Jumma’ah a Masallatan da suka fi kusa da gidajensu don kaucewa shiga tsananin rana. 

Don haka Ma’aikatar Aikin Hajji ta Kasar Najeriya na kara jaddada ayi anfani da wannan nasihar ta yin Salla a Masallatai Mafiya kusa da Masaukan Alhazanmu.

Sanarwar wacce babban jami'in hukumar NAHCON dake Makkah, Dr Ibrahim Muhammad Sodangi ya sanyawa hannu, ta yi fatan Alhazan zasu yi amfani da wannan shawara ta kwararru da aka domin kaucewa shiga babbar matsala 

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki