Dalilin Da Zan Koma Daura Idan Na Bar Mulki —Buhari


Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, ya ce zai koma Daura da zarar ya kammala wa’adin mulkisa don guje wa matsaloli.

Shugaban ya bayyana haka ne a ranar Lahadi lokacin da ya karbi bakuncin mazauna Babban Birnin Tarayya don ta su murnar bikin Kirsimeti.

Kazalika, Buhari ya gode wa ’yan Najeriya da suka yarda tare da amince masa ya shugabance su.

Ya ce duk da ci gaba da aka samu a fasaha da kimiyya, hankalinsa zai fi kwanciya idan ya koma garinsa.

Buhari dai ya jima da cewa da zarar ya kammala wa’adin mulkinsa zai bar Abuja gaba daya, don kauce wa shiga sabgogin gwamnatin da za ta gaje shi.

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki