Search This Blog

Sunday, 25 December 2022

Dalilin Da Zan Koma Daura Idan Na Bar Mulki —Buhari


Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, ya ce zai koma Daura da zarar ya kammala wa’adin mulkisa don guje wa matsaloli.

Shugaban ya bayyana haka ne a ranar Lahadi lokacin da ya karbi bakuncin mazauna Babban Birnin Tarayya don ta su murnar bikin Kirsimeti.

Kazalika, Buhari ya gode wa ’yan Najeriya da suka yarda tare da amince masa ya shugabance su.

Ya ce duk da ci gaba da aka samu a fasaha da kimiyya, hankalinsa zai fi kwanciya idan ya koma garinsa.

Buhari dai ya jima da cewa da zarar ya kammala wa’adin mulkinsa zai bar Abuja gaba daya, don kauce wa shiga sabgogin gwamnatin da za ta gaje shi.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

KNSG Declares Tuesday,1st September, 2026, A Public Holiday

Kano State Government has declared Tuesday, 1st September, 2026, corresponding to 19th Rabi’ul Awwal, 1448 AH, a public holiday ...