Search This Blog

Thursday, 11 January 2024

Bom Ya Kashe Mutane 8, Wasu Dama Sun Jikkata A Borno

 


Akalla mutane takwas ne ake fargabar sun mutu sakamakon fashewar wasu bama-bamai a kan hanyar Ngala zuwa Dikwa a Karamar Hukumar Ngala a Jihar Borno.

Rahotannin sun nuna cewar, mutane da dama sun samu raunuka a sakamakon tashin bom din a kauyen Kinewba a ranar Talata.

Wata majiyar tsaro ta ce “Akalla Mutane  8 ne ake fargabar sun mutu, ciki har da yara biyu, sannan wasu da dama sun samu munanan raunuka sakamakon fashewar nakiyoyin.”

Majiyar ta ce fashewar bom din ya yi kaca-kaca da wasu motocin biyu yaddda ba za a iya gyara su ba.

Wata babbar majiya ta jami’an farin kaya na  JTF ta ce motocin biyu kirar Isuzu da wata babbar mota ce suka taka bom din kuma ana fargabar kashe kusan dukkan fasinjojin ciki.

“Wadannan motocin dai sun bar garin Ngala da misalin karfe 9 na safe, yayin da lamarin ya faru a nisan kilomita 15,” in ji majiyar.

Majiyarmu ya ruwaito cewa, tashin bama-baman ya faru ne a tazarar kilomita 15 daga Maiduguri, babban birnin jihar.

(AMINIYA)

Wednesday, 10 January 2024

Yanzu-Yanzu: Shugaba Bola Ahmed Tinubu Ya Nada Sababbin Shugabannin Hukumar NAHCON

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da nadin sababbin 'yan hukumar gudanarwa na hukumar alhazai ta kasa (NAHCON), har sai majalisar dattawan Najeriya ta tabbatar da hakan.


A sanarwar da mai taimakwa Shugaban kasar kan harkokin kafafen yada labarai, Ajuri Ngelale ya sanyawa hannu, yace Shugaban a cikin kudurinsa na tabbatar da gudanar da aikin Hajji na shekarar 2024 ba tare da matsala ba, ya nada wadannan mutane a Hukumar NAHCON:

Jalal Arabi - Shgaba 

Aliu Abdulrazaq - Kwamishinan tsare-tsare, Ma'aikata, da Harkokin Kudi

Prince Anofi Elegushi - Kwamishinan Ayyuka

Professor Abubakar A. Yagawal - Kwamishinan Tsare-tsare & Bincike

Wakilan shiyya: 

Dr. Muhammad Umaru Ndagi — Arewa ta tsakiya

Abba Jato Kala — Arewa maso gabas 

Sheikh Muhammad Bin Othman - Arewa maso Yamma

Tajudeen Oladejo Abefe - Kudu maso Yamma

Aishat Obi Ahmed — Kudu maso Gabas

Zainab Musa – South South

Professor Musa Inuwa Fodio — Jama’atul Nasril Islam

Farfesa Adedimiji Mahfouz Adebola — Majalisar Koli kan Harkokin Musulunci

Shugaban ya umurci wadanda aka nada su sadaukar da kansu wajen ganin cewa ayyukan hukumar alhazai ta kasa sun kasance masu inganci da gaskiya da kuma biyan bukatun ‘yan Najeriya.


Shugaban NAHCON Ya Nemi A Sake Inganta Ayyukan Da Ake Yi Wa Alhazan Najeriya

A ziyarar da ya kai a jiya, 9 ga watan Janairu, 2024, a bankin ci gaban Musulunci, Shugaban Hukumar Hajji ta kasa, Malam Jalal Ahmad Arabi, ya nemi a karfafa alaka da bankin ci gaban Musulunci. 

A sanarwar da mataimakiyar daraktar harkokin hulda da jama'a da dab'i ta hukumar, Fatima Sanda Usara ta sanyawa hannu, tace shugaban ya mika godiyarsa ga Mataimakin Shugaban Ayyuka Dr Mansur Mukhtar, bisa tallafin fasaha da NAHCON ta samu a shekarar 2019 wanda ya taimaka wa dalibai da kafa tsarin ceton Alhazai da Cibiyar Hajji ta Najeriya. ( Karin bayani kan ziyarar bankin raya Musulunci za ta biyo baya).
 
Shugaban ya gabatar da bukatar daukar nauyin kwararrun ma’aikatan Najeriya irin su Likitocin dabbobi, ma’aikatan don bayar da ayyuka a lokacin aikin Hajji musamman a karkashin Hadaya. 

Haka kuma ya bukaci Bankin ya bude wa Najeriya kasuwa don fitar da dabbobin hadaya da sauransu.

Malam Jalal Ahmad Arabi a yau 10 ga watan Junairu 2024 ya ci gaba da leko tare da tantance wasu masu gudanar da ayyuka don shiga hidimar alhazan Najeriya a inda ya dace. Ya ziyarci sauran mahajjata’ Muttawif Establishments don nazarin ayyukan da ke cikin tsarinsu. 

Ma'aikatar Hajji da Umrah ta Saudiyya ta samar da dama ga kasashe don zabar Kamfanonin Mutawwif na Alhazai da suke so a matsayin hanyar karfafa hidimar Alhazai da ta dace. 
 
A baya shugaban ya tuntubi Dr Abdulrahman Bejawi, mataimakin ministan aikin hajji mai kula da aikin umrah da ziyara a Madina. A can, ya nemi jajircewa kan batutuwan da suka shafi jin dadin alhazan Najeriya da kare dukiyoyinsu. 

Haka kuma Malam Arabi ya yi na'am da aikin hanyar Makkah da mataimakin ministan ya bayar, Najeriya na daya daga cikin kasashe bakwai da suka bayar da ayyukan. A cewar Dr Bejawi, sama da kasashe 30 ne suka nuna sha'awar wannan shirin.
 
Malam Jalal Arabi ya rattaba hannu kan yarjejeniyoyin da aka kulla da Janar Car Syndicate, Ofishin Jakadancin United Agents da kuma Adillah Establishment of Madinah.

Gwamna Umar Namadi Ya Nada Sabon Darakta Janar Na Hukumar Alhazai Ta Jigawa

Gwamna Malam Umar A. Namadi ya amince da nadin Ahmed Umar Labbo a matsayin Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa na tsawon shekaru hudu.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun sakataren gwamnatin jihar Jigawa Malam Bala Ibrahim.

Sanarwar ta ce nadin Labbo a matsayin Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa an yi shi ne bisa cancanta

Malam Bala Ibrahim ya bayyana cewa, Ahmed Umar Labbo ya yi aiki a matsayin Darakta aiyuka na hukumar kuma an daukaka shi zuwa matsayin babban sakataren hukumar a ranar 20 ga Maris, 2023 bisa la’akari da kwarewarsa da kuma tarihin aikinsa.

“Saboda haka, muna fatan wanda aka nada zai tabbatar da amincewar da aka yi masa, ya kuma yi iya kokarinsa wajen ci gaban jihar Jigawa,” in ji SSG.

Sanarwar ta bayyana cewa, nadin zai fara aiki daga ranar 11 ga watan Janairu, 2024

Bakuwa Ta Sace Jariri Awa 3 Da Haihuwarsa A Asibiti

 Ana zargin bakuwa ta sace jaririn ne da hadin bakin ’yar uwar mai jegon


Wata mata ta sace jariri awa uku bayan haihuwarsa a Asibitin Kwararru na Dalhatu Arafat (DASH) da ke garin Lafia, Jihar Nasarawa.

Ana zargin bakuwar ta sace jaririn ne da hadin bakin ’yar uwar mai jegon sa’o’i kadan da haihuwarsa ta hanyar yi wa mahifiyarsa tiyata.

Aminiya ta gano bayan haihuwarsa da misalin karfe 3 na asubahin ranar Talata ne jami’an asibiti suka mika jaririn da mai jegon ga wata ’yar uwarta domin ta ci gaba da kula da su.

Wani ganau da ya nemi a boye sunasa ya ce, bayan sun dawo dakin masu jego ne ’yar uwar mai jegon ta kawo mata da wata bakuwa, wadda ake zargin sun hada baki wajen sace jaririn.

‘Kamar Layar Zana’

A cewarsa, “’yar uwar mai jegon ce ta ce mata za ta koma gida ta dauko cajar wayarta da ta manta; shi ne ta hada ta da wata mata da za ta zauna da su kafin ta dawo ,” wadda ake zargin ita ce ta sace jaririn.

Sace jaririn daga dakin masu jegon da misalin karfe 6 na safe,  awa uku da haihuwarsa ya jefa daukacin jami’ai da sauran mutanen asibitin cikin al’ajabi.

Wata ’yar uwar mai jegon da ta nemi a boye sunanta, ta tabbatar cewa, ’yar uwarsu ce kawo wa mai jegon wata bakuwa, ta kuma damka mata jaririn.

A cewarta, ba su yi aune ba, sai dai aka nemi jaririn da bakuwar — wadda ya yi zargin matsafiya ce — suka rasa, sun yi layar zana.

Ta ce, “Ba mu ga barauniyar jaririn ba, wannan wane irin rashin imani ne, mace ta shiga asibiti ta yaudari duk ’yan dakin da masu tsaron kofa cewa za ta yi masa wanka, amma ta tsere da jariri. Duniya ta zama abin tsoro!”

Yadda Aka Sace Jaririna —Mai Jego

Mai jegon, Malama Wasira Suleiman, wadda ke zubar da hawaye, ta ce “wadda aka kawo domin ta taimaka wajen kula da jaririn, ita ce ta sace jaririn da na dauka a cikina wata tara.”

Malama Wasira ta roki Gwamnatin Jihar Nasara da hukumar gudanarwar Asibitin DASH da hukumomin tsaro su taimaka su ceto jaririn nata ba tare da komai ya same shi ba.

Mahaifiyar jaririn ta bayyana cewa, “saboda ba ni da karfin da zan iya yi wa kaina komai” aka kawo matar a matsayin ’yar aike — idan mai jegon tana bukatar wani abu, ko sayen magunguan idan an bukaci hakan.

mma duk da haka matar ta nace cewa tana da kayan da za a lullube shi idan aka yi wankan, a karshe da mai jegon ta amince matar ta yi masa wanka, sai daga baya aka ce mata a sace jaririn nata.

“Wahalar da na sha na wata tara ba shi da misali, don haka babu abin da za a fada min da zan hakura; karfe biyun dare aka yi mini tiyata fa,” in ji mai jegon.

Bai Taba Faruwa Ba  —Hukumar Asibiti

Mukaddashin Shugaban Sashen Kula da Masu Juna Biyu na Asibitin DASH, Dalhatu Arafat ya bayyana takaicinsa kan lamarin yana mai cewa haka bai taba faruwa a asibitin ba.

A cewarsa, bayan an yi wa mai jegon aiki ta haihu da misalin karfe 3 na asubahin Talata aka kai ta dakin masu jego tare da mai kula da it.

Ita kuma ta kawo wata bakuwar da ba ta sani ba domin kula da su, za ta  je gida ta dauko wani bu.

“Abin takaici, bakuwar ta dauki jaririn da cewa za ta yi masa wanka, daga nan ta yi layar zana da shi, abin da mu a asibitin muka sani ke na,” in ji shi.

Amma ya ce duk wadanda ke da alaka da sace jaririn sun hannun ’yan sanda ana bincike domin gano bakuwar da ta sace jaririn.

Dalhayu Arafa ya ce, “sai da muka kira kowa, saboda wannan ne karo farko a haka ya faru a nan” kuma wadanda aka kama sun hada da ’yar uwar mai jegon da ta kawo bakuwar da wasu ma’aikatan asibitin da ke aiki a lokacin da abin ya faru.

Duk wanda aka samu da hannu za mu sallame shi mu mika shi ga hukuma, domin zama darasi ga masu irin wannan hali.

“Za kuma mu kara amfani da kyamarorin CCTV domin daukar duk wani motsi a cikin dakunan marasa lafiya,” in ji shi.

(AMINIYA)

EFCC Ta Kwace Fasfon Sadiya Da Betta Edu


Hukumar Yaki da Masu yi wa Tattalin Arzikin Kasa Zagon Kasa (EFCC), ta kwace fasfo din tsohuwar Ministar aJin-kai, Betta Edu da magabaciyarta, Sadiya Umar-Farouq, kan binciken badakalar da ake yi a ma’aikatar.

Wata majiya mai tushe daga EFCC ta ce an kwace fasfo din Edu da da Sadiya ne domin hana su fita daga Najeriya yayin da ake ci gaba da binciken.

“Hukumar ta kwace fasfo din tsofaffin ministocin biyu, Sadiya Umar-Farouq da Betta Edu.

“Mun kuma kwace fasfo din Halima Shehu har sai an kammala bincike. Hukumar ba ta son yin kasadar ganin ko daya daga cikinsu ya fice daga Najeriya alhalin ana bincike a kan su,” in ji majiyar.

Dangane da binciken Edu da Sadiya Umar-Farouq, EFCC ta gayyaci shugabannin bankunan Zenith, Providus da Jaiz ofishinta a ranar Talata.

Ita ma Halima Shehu, wacce aka dakatar daga hukumar kula da harkokin zuba jari ta kasa, EFCC na bincike a kan ta.

Aminiya ta ruwaito cewa Edu ta isa hedikwatar EFCC da misalin karfe 10 na safiyar ranar Talata domin amsa tambayoyi kan zargin almundahanar kudi da ake mata.

Wannan na zuwa ne bayan fitar wata takarda da ta nuna cewa Edu ta bukaci babban Akanta-Janar na Tarayya ya biya Naira miliyan 585 da aka ware wa marasa galihu zuwa wani asusun banki na daban.

A nata bangaren kuma, Sadiya Umar-Farouq, tsohuwar minista a lokacin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, ita ma EFCC ta gayyace ta domin amsa tambayoyi kam zargin da ake mata na sama da fadi da sama da biliyan 37.

(AMINIYA)



Monday, 8 January 2024

Labari Da Dumiduminsa: Shugaba Bola Ahmed Tinubu Ya Dakatar Da Ministar Harkokin Walwala Betta Edu

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya dakatar da ministar jin ƙai, Betta Edu nan take.

Kakakin shugaban Najeriyar, Ajuri Ngelale ne ya sanar da matakin dakatar da ministar cikin wata sanarwa da aka fitar a yau.

Shugaba Tinubu ya ɗauki matakin ne domin ba da dama ga hukumar EFCC mai yaƙi da cin hanci da rashawa ta gudanar da bincike a kanta.

Tun farko al'ummar Najeriya sun yi ta matsa lamba inda suke kiraye-kiraye gwamnati ta dakatar da ita daga mukaminta domin a gudanar da cikakken bincike a kanta game da zarge-zargen da ake mata.

Ana zargin ta da bayar da umarnin tura kuÉ—i kimanin naira miliyan 585 zuwa asusun bankin wata mata.

(BBC HAUSA)

Sunday, 7 January 2024

Najeriya da Saudi Arabiya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna kan aikin hajjin 2024


A yau 7 ga watan Junairu 2024 ne Najeriya karkashin hukumar alhazai ta kasa NAHCON ta amince da gudanar da aikin Hajjin bana ta hanyar rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna ta shekarar 2024 (1445AH) da ma'aikatar aikin hajji da umrah ta kasar Saudiyya.


A sanarwar da mataimakiyar daraktar harkokin hulda da jama'a da dab'i ta hukumar, Fatima Sanda Usara ta sanyawa hannu, tace bikin rattaba hannun da aka yi a Jeddah ya samu halartar manyan wakilai daga Najeriya karkashin jagorancin ministan harkokin wajen Najeriya Ambasada Yusuf Maitama Tuggar da Malam Jalal Ahmad Arabi, mai rikon mukamin Shugabancin NAHCON. 

Tawagar kasar Saudia ta samu jagorancin Ministan Hajji da Umrah na Saudiyya, Dr. Taufiq Al-Rabiah.
 
 
Kafin rattaba hannu kan yarjejeniyar, Ministocin biyu sun yi wata ‘yar gajeruwar tattaunawa inda Najeriya ta bukaci a kawo karshen matsalar karancin tantuna a Mina tare da neman karin wasu sharuddan da suka dace ga dilolin Najeriya a lokacin jigilar kayayyaki. Tawagar ta Najeriya ta kuma gayyaci Ministan Hajji da Umrah da ya ziyarci Najeriya.
 
 
A nata jawabin, ministar Saudiyya, Dakta Rabiah, ta amince da kalubalen da ke tattare da sararin samaniya a Mina, ta kuma ba da tabbacin cewa, ana kokarin inganta amfani da murabba'in Miliyan biyu ga mahajjata sama da miliyan biyu da ke aikin Hajji a duk shekara. 

Ya bayyana goyon bayan ma’aikatar ga dukkan matakan da suke da shi na baiwa alhazai kyakkyawar hidima. Dr Rabiah ta yarda ta ziyarci Nigeria nan ba da dadewa ba.
 
Sauran mahalarta taron daga Najeriya sun hada da karamin jakadan Najeriya a Jeddah, Amb. Bello Hussaini Kazaure, manyan hafsoshi daga Ofishin Jakadancin Najeriya a Saudiyya da NAHCON.
 

Friday, 5 January 2024

Labari Da Dumiduminsa: Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Kamfanonin Jiragen Da Zasu Yi Jigilar Maniyyata Hajin 2024

Gwamnatin tarayyar Najeriya karkashin jagorancin shugaba Bola Ahmed Tinubu ta amince da wasu manyan kamfanonin jiragen sama guda uku da za su yi jigilar maniyyata aikin hajjin 2024, wadanda suka hada da Air Peace., FlyNas da Max Air. 

Har ila yau, an amince da wasu kamfanoni uku na jigilar kayayyaki da za su yi jigilar kayan alhazai WaÉ—annan su ne Cargo Zeal Technologies Ltd, Nahco Aviance da Qualla Investment Limited.
 
A sanarwar da mataimakiyar daraktar harkokin hulda da jama'a da dab'i ta hukumar, Fatima Sanda Usara ta sanyawa hannu, tace Yarjejeniyar ta karfafa yunÆ™urin gwamnati na tabbatar da ingantaccen aikin hajji ga maniyyatan Najeriya. 

Don haka, a lokaci guda gwamnatin tarayya ta amince da rabon maniyyata daga jahohi daban-daban ga kowane kamfanonin jiragen sama da aka amince da su kamar haka:
 
i.Air Peace zai yi jigilar maniyyata daga: Abia, Akwa Ibom, Anambra, Bayelsa, Cross River, Delta, Ebonyi, Edo, Ekiti, Enugu, FCT, Imo, Kwara, Ondo da Ribas.
ii.FlyNas za ta yi jigilar alhazai musulmi daga: Borno, Lagos, Osun, Ogun, Niger, Sokoto, Kebbi, Yobe da Zamfara.

iii. Kamfanin Max Air da ke da kaso mafi tsoka ne zai dauki nauyin jigilar alhazai daga: Bauchi, Benue, Kano, Katsina, Kogi, Nasarawa, Adamawa, Oyo, Taraba, Kaduna, Sojoji, Gombe, Jigawa da Plateau.
 
Rabon maniyyatan ga kamfanonin jirage ya yi daidai da yarjejeniyar da aka cimma tsakanin Najeriya da Saudiyya kan jigilar alhazai a karkashin kason gwamnati. 

A wani labarin kuma, Ministan harkokin wajen Najeriya Ambasada Yusuf Maitama Tuggar na shirin jagorantar wata tawaga daga hukumar alhazai ta kasa NAHCON domin halartar rattaba hannu kan yarjejeniyar aikin hajjin shekarar 2024. a wannan wata na janairu
 
Malam Arabi ya taya murna kamfanonin jiragen sama da aka amince da su a kan zaben da aka yi musu, ya kuma yi kira gare su da su tashi tsaye wajen gudanar da aikin hajji cikin kwanciyar hankali a kakar 2024. Hukumar NAHCON ta ci gaba da sadaukar da kai wajen tabbatar da mafi girman matsayi a harkar aikin hajji, tare da mai da hankali kan aminci da gamsuwar mahajjata.
 

Tuesday, 2 January 2024

Labari Da Dumiduminsa: Hukumar NAHCON Ta Kara Wa'adin Biyan Kudin Aikin Hajji Bana

Dangane da koke-koken da malaman addini, hukumomin jin dadin alhazai Jiha, Gwamnonin Jihohi da sauran masu ruwa da tsaki suka gabatar dangane da rufe rajistar aikin hajjin 2024, Hukumar Alhazai ta Najeriya (NAHCON) ta yi farin cikin sanar da amincewar gwamnatin tarayya. don tsawaita wa'adin. 

A sanarwar da mataimakiyar daraktar harkokin yada labarai da dab'i ta Hukumar, Fatima Sanda Usara ta sanyawa hannu, tace daga yanzu an mayar ranar wa'adin zuwa  Janairu 31, 2024, yana ba da Æ™arin dama ga daidaikun mutane su samu damar zuwa aikin Hajji 
 
 
Bukatar neman tsawaita lokacin daga al'ummomin addinai daban-daban na nuna muhimmancin tabbatar da yadda dimbin masu kishin addinin ke da sha'awar shiga aikin Hajji.
 
Don haka, NAHCON na da yakinin cewa kafin cikar wa’adin, tare da tallafin Hukumomin Alhazai na Jahohi ta zasu fitar da jimillar kudin aikin Hajjin 2024. 

Don haka tsawaita wa’adin ya samar da kofa ga sabbin masu rajista don yin hakan kuma a karshen watan Janairu, wadanda ke bukatar daidaita kudadensu ma za su iya yin hakan.
 
Hukumar NAHCON ta yi amfani da wannan dama wajen tunatar da maniyyata da sauran masu ruwa da tsaki cewa ma’aikatar aikin Hajji da Umrah ta Saudiyya ta sanya ranar 25 ga watan Fabrairu a matsayin karshen sanya hannu kan duk wasu kwangiloli, wanda ke nuni da kawo karshen biyan kudaden da ake biya a asusun IBAN. 

Da wannan tsawaita wa’adin, NAHCON ya rage wata guda kafin ta kammala biyan dukkan kudaden da suka ajiye a asusunta na IBAN na aikin Hajjin 2024.
 
Wannan karin wa’adin, duk da cewa ya zarce wa’adin shirye-shiryen NAHCON, ya nuna yadda Shugaban Hukumar, Malam Jalal Ahmad Arabi ya jajirce wajen ganin an shawo kan matsalolin masu ruwa da tsaki. Ya kuma mika godiyarsa ga malaman addini, shuwagabannin hukumomin jiha, da gwamnoni bisa yadda suka bayar da shawarar a madadin mahajjatan. 

Malam Arabi ya bayyana wannan kokari na hadin gwiwa a matsayin shaida na sadaukarwar da aka yi na sauwaka ma’ana da sanin makamar aikin Hajji ga kowa da kowa. Ya yi addu’ar duk masu gudanar da aikin Hajji za su yi amfani da wannan damar da kyau don samun nasarar ayyukan Hajji na 2024.
 
 

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

IHRC-RFT Nigeria Expresses Concern Over the Increasing Cross-Border Movement of Pastoralists and Their Livestock

The International Human Rights Commission – Relief Fund Trust (IHRC-RFT) Nigeria Chapter, an organization with Special Consultat...