Gwamnat Jihar Kano Ta Sanar da Hutun Babbar Sallar Ga Dukkan Makarantun Gwamnati da Masu Zaman Kansu


Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kano ta sanar da hutun Sallar Idin Kabir ga dukkan makarantun firamare da sakandire na gwamnati da masu zaman kansu a fadin jihar.

A cikin wata sanarwa da Daraktan Wayar da Kai na Ma’aikatar, Musbahu Aminu Yakasai ya fitar, an umarci dukkan makarantun kwana da su tafi hutun Sallah daga ranar Asabar, 23 ga Mayu, 2026, sannan su koma makaranta ranar Lahadi, 31 ga Mayu, 2026.

Haka kuma, makarantun jeka-ka-dawo za su fara hutun Sallah daga ranar Juma’a, 22 ga Mayu, 2026, sannan su koma makaranta ranar Litinin, 1 ga Yuni, 2026.

An shawarci iyaye da masu kula da daliban makarantun kwana da su je su karÉ“i ’ya’yansu a ranar rufe makaranta da aka amince da ita, wato Asabar, 23 ga Mayu, 2026, tare da tabbatar da dawo da su a kan lokaci ranar komawa makaranta.

Kwamishinan Ilimi, Gwani Dakta Ali Haruna Abubakar Makoda, ya yi fatan alheri ga dalibai, malamai, iyaye da daukacin al’ummar bangaren ilimi, tare da yi musu fatan gudanar da bukukuwan Sallar Idin Kabir cikin zaman lafiya da annashuwa.

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki