Search This Blog

Sunday, 2 April 2023

Yanzu-Yanzu : Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Mika Mulki Mai Dauke Da Mutum 17

Majalisar zartaswar jihar Kano ta amince da kafa kwamitin mika mulki mai mambobi 17 domin mika mulki ga gwamnati mai jiran gado a jihar.

Majalisar ta kuma amince da wani karamin kwamiti mai mutum 100 wanda za a fitar da kundin tsarin kunshinsa daga ma’aikatu da ma’aikatu da hukumomi daban-daban (MDAs).

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida na jihar, Malam Muhammad Garba, wanda ya tabbatar da wannan batu a lokacin da yake zantawa da manema labarai kan sakamakon taron majalisar na mako-mako da aka gudanar a zauren majalisar da ke gidan gwamnatin jihar Kano, ya ce ana sa ran zababben gwamnan zai ba da wakilai uku a babban kwamitin.

Ya ce kwamitin wanda ke karkashin jagorancin sakataren gwamnatin jiha Alhaji Usman Alhaji yana da wadannan mambobi a matsayin shugaban ma’aikatan gwamnati, babban lauya/kwamishanan shari’a, kwamishinan yada labarai, kwamishinan muhalli, kwamishinan kasuwanci. , Masana'antu da HaÉ—in kai.

Sauran sun hada da kwamishinan tsare-tsare da kasafin kudi, kwamishinan kananan hukumomi, kwamishinan ayyuka da samar da ababen more rayuwa, kwamishinan kudi, kwamishinan ilimi, darakta-janar, ofishin kula da filaye, darakta-janar, bincike da takardu, Manajan Darakta na hukumar tsara Birane da sauransu. Hukumar Raya Kasa, yayin da Babban Sakatare, Binciken Bincike da Harkokin Siyasa, REPA za ta zama sakatariyar kwamitin.

Malam Garba ya bayyana cewa, babban kwamatin zai yi aiki cikin jituwa da nufin rubutawa tare da mika rahoton mika mulki na karshe cikin makonni uku.

Kwamishinan ya bayyana cewa an ba wa babban kwamitin rikon kwarya umarnin fara shirin mika mulki tare da rubuta nasarorin da aka samu a cikin wa’adin mulki biyu na gwamnatin Gwamna Abdullahi Umar Ganduje.

Ya ce kwamitin zai kuma samu tare da tantance rahotanni daga ma'aikatu da sassan gwamnati ta fuskar manyan ayyuka

Saturday, 1 April 2023

Lawan Majakura: Mai Sayar Da Kifi Da Ya Kada Shugaban Majalisar Yobe

 


A zaben Gwamna da na ’yan majalisar jiha da aka gudanar a ranar Asabar 18 ga Maris ne Lawan Musa Majakura mai shekara 33, ya kayar da Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Yobe, Alhaji Ahmed Mirwa Lawan da kuri’a 182 don wakiltar Mazabar Nguru II a Karamar Hukumar Nguru a Jihar Yobe.

Majiyarmu ta tattauna da zababben dan majalisar na Jam’iyyar PDP ta waya, inda ya yi bayani kan takaitaccen tarihi da harkokin siyasarsa da yadda ya samu nasarar da ta yi waje da Shugaban Majalisar:

Mene ne takaitaccen tarihinka?

An haife ni a garin Majakura da ke Karamar Hukumar Nguru a watan Janairun 1990. Na yi karatun firamare a Majakura.

Daga nan na wuce Kwalejin Gwamnati da ke Nguru, inda na samu karamar Diploma a Nazarin Addinin Musulunci.

Daga nan na tafi Kwalejin Kimiyya da Sana’a ta Tarayya da ke Damaturu, inda na kammala a shekarar 2009 tare da samun takardar Babbar Diploma (HND) a fannin kasuwanci da Gudanarwa a 2020.

To amma ban samu damar yi wa kasa hidima ba (NYSC) saboda shekaruna sun zarta shi ya sa na samu takardar shaidar yawaitar shekaru kamar yadda tsarin hakan ya nuna.

Daga nan ne na tsunduma cikin harkar sayar da kifi da sauran abubuwan da za su ba ni wani abu don ci gaba da bukata ta.

A halin yanzu ina da mata daya da ’ya’ya hudu.

An zabe ka dan Majalisar Dokokin Jiha, ko ka taba tsayawa takarar wani mukami?

Eh, lallai na taba tsayawa takarar kansila a 2021 lokacin ina Jam’iyyar APC kafin in koma PDP, amma ban samu ba.

Mutanenmu musamman matasa, sun ce in yi takara, domin suna ganin zan iya yin abin da ya fi haka, amma Allah bai Sa na dace ba a wancan lokaci, daga bisani muka yi addu’ar Allah Ya ba mu matsayi mafi alheri da za mu taimaki al’umma.

Alhamdulillah Allah kuwa Ya karbi addu’armu da na manyanmu ga shi yanzu na zama dan majalisar dokoki.

Kamar yadda muka samu labari a baya an ce akwai lokacin da wasu jami’an tsaro suka kama ka, kuma suka tsare har sau uku saboda sukar shugaban majalisar da wasu ’yan siyasa a Facebook. Mece ce gaskiyar hakan?

A gaskiya an kama ni sau biyu. Daya daga cikinsu ya fito daga wani dan siyasa a Jam’iyyar APC kafin in bar jam’iyyar, bayan na yi masa suka a Facebook, sai ’yan sanda su kama ni suka tsare ni na tsawon kwana biyar.

Na biyu shi ne na Shugaban Majalisar wanda na yi suka a kan rashin wakilci nagari da yake mana mu al’ummar Mazabar Nguru 11.

An kama ni aka tsare na tsawon awa 48 wato a bara a cikin watan Ramadan wato kamar yanzu.

Kuma abin da ke jawo min irin wannan kamu bai wuce duk lokacin da na ji cewa gwamnatin jiha ta amince da aikin mazabu ga ’yan majalisar jiha, nakan tabbatar da inda aka kashe namu kudaden, idan yana da wani tasiri a cikin al’ummarmu, inda nakan bi diddiginsu don ganin an yi aikin.

Don haka matukar na ga ya gaza yin abin da ya dace nakan soke shi a duk lokacin da na gano cewa muna da matsalar da zai iya magancewa amma ya kasa yin haka, kuma nakan yi suka ce ta gaskiya babu son zuciya a ciki hakan ke haifar min da kamu da tsarewa.

Me ya jawo hankalin ka, ka tsaya takara da Shugaban Majalisar wanda ya shafe shekara 20 a majalisar har ya kai matsayin da yake kai a yanzu?

Hakikanin gaskiya abubuwa da yawa sun yi tasiri kan tsayawa takararta.

Abu na farko, fannin ilimi, muna da komawa baya a kauyenmu na Majakura kuma mukan ga yadda abubuwa suke faruwa kowace rana inda ajujuwanmu sun lalace ga kuma karancin ayyukan yi ga matasanmu masu yawa haka nan a bangaren lafiya nan ma haka lamarin yake don haka na gane cewa rashin wakilci mai kyau ya haddasa mana shiga cikin wannan yanayi.

Don haka don magance wadannan kalubale ne, ya sa mutanenmu suka ce in tsaya takara watakila suna tunanin zan yi abubuwa daban da za su taimaka musu.

Ka ce mutanenka suka ce ka fito takara, ko sun ba ka wani tallafi don yakin neman zabe?

Eh, sun saya min fom din takara. Sun kuma ba da gudunmawar kudi don yakin neman zabe kuma ba su tuntube ni ba ko ina da sha’awa ko a’a.

Sai kawai suka sayi fom suka ce suna so in tsaya takara, ni kuma ban tambaye su nawa suka sayi fom din ba, nan take na cika na mayar musu da shi.

Ka san cewa lokacin da kake neman kujera a kowace jam’iyya akwai zaben fid-da gwani, amma na yi nasara ba tare da hamayya ba a jam’iyyata ta PDP.

Mutanen kauyena wadanda galibi manoma ne da masu sayar da kifi, su ma sun tara min kudi don yakin neman zabe cikinsu akwai wadanda sukan kira ni ta waya suna yi min fatar samun nasara, wasu kuma su tura Naira dubu 20 zuwa dubu 50 a asusun bankina, duk don suna ganin zan iya yin abubuwan da suka dace matukar na kai ga nasara.

A lokacin yakin neman zabenmu, an yi ta tursasa wa mutane saboda bambancin jam’iyya, amma alhamdulillahi duk da kalubalen da aka fuskanta mun samu nasarar cin zabe, amma dai ba abu ne mai sauki ba kayar da Shugaban Majalisar Dokoki ta Jiha.

Ko Shugaban Majalisar ya tuntube ka kafin zabe a kan ka janye masa?

Maganar gaskiya bai tuntube ni don in janye takararta shi da kansa ba. Amma wani jami’in gwamnati da wasu da nake tunanin wakilansa ne sun zo min sau biyu suna cewa in janye.

Sun yi alkawarin ba ni Naira miliyan 18, amma na ki, daga baya suka dawo suka yi min tayin Naira miliyan100, amma na ki.

Na ce da su mutanen kauyenmu ne suka sayo min fom don tsayawa takara saboda sun yi imanin cewa zan yi abubuwan da suka kamata in na samu nasara.

Don haka ban ga dalilin da zai sa in janye daga takara ba. Da na ga sun matsa sai na ce su je su hadu da mutanena idan da gaske suna son in janye takarata ga duk wanda ya aiko su gare ni.

Daga bisani na gaya wa jama’ata abin da muka tattauna amma duk mun yarda cewa ba zan janye ba, sai muka ci gaba da yakin neman zabe ba tare da sake saurararsu ba.

Wane abu za ka sa gaba in ka shiga majalisa domin al’ummar mazabarka?

A koyaushe muna yin abubuwa daban misali, kamar yadda nake magana da ku, ina da ’yan mata sama da 25 da maza 30 da suka samu karatun sakandare ta hanyar tallafi da horarwa.

Shugaban Majalisar ba zai iya gaya muku adadin mutanen da ya taimaka wajen cimma wannan buri ba kasancewar ban yi tsammani yana da abin fada ba kan haka.

Dangane da kyakkyawan wakilci, zan ba da fiffiko ga ilimi ta hanyar gyara azuzuwanmu tare da tabbatar da mun dauki kwararrun malamai da samar da kayan koyo da koyarwa.

Na biyu, cibiyoyin kula da kiwon lafiyarmu suna bukatar kulawa sosai ta hanyar samar da magunguna da ma’aikatan lafiya kwararru lura da cewa muna da al’ummomi masu yawa.

Har ila yau zan kokarta wajen samar da ruwa da kuma sauran kayan more rayuwa.

Haka nan zan matsa ta wajen rokon gwamnati ta yi wa mutanenmu abubuwan da suka dace na ci gaban su, kuma zan yi duk mai yiwuwa wajen gabatar da kudiri don tabbatar da cewa an sake gina hanyoyinmu da suka lalace a mazabata in Allah Ya so.

Akwai mutane da dama da suka kammala karatu amma ba su da aikin yi kuma makarantunmu na bukatarsu, don haka zan tabbatar da cewa gwamnati ta dauki irin wadannan mutanen aiki, walau aiki na wucin-gadi ko na dindindin.

Zan tabbatar cewa ina tare da mutanena a kowane karshen mako don jin matsalolinsu da abin da zan iya yi don magance su.

Idan ba zan iya magance matsalolin ba zan kai su ga bangarorin da suka dace don daukar mataki a kai.

Gwamna Buni ko Shugaban Majalisar akwai wanda ya kira ka don taya ka murnar lashe zabe?

Gaskiya babu daya daga cikinsu da ya kira ni ya taya ni murna, amma na samu sakonnin taya murna daga ma’aikatan gwamnati da ’yan siyasa da ’yan jarida da kuma kungiyoyin farar hula.

Sakonnin wadannan mutane sun karfafa ni, don haka ban damu da sakon Shugaban Majalisar ba.

Sakamakon zaben ya nuna Jam’iyyar APC na da kujerun ’yan majalisa 22 yayin da jam’iyyarku ta PDP ke da biyu, ku ’yan tsiraru ne da hakan na iya shafar aikinku, ko akwai yiwuwar ku sauya sheka zuwa APC?

A gaskiya ba zan ce komai ba domin Allah ne kadai Ya san abin da zai faru yau ko gobe, Na san cewa Gwamna Buni mutum ne mai tawali’u mai basirar shugabanci, don haka bisa fahimtata da shi ba zai bari bambancin jam’iyya ya yi tasiri ga ci gaban Nguru ko Jihar Yobe ba.

Abin da zan iya cewa shi ne, zan yi duk mai yiwuwa don ganin na isar da sako da matsalolin al’ummar mazabata wadanda aka bari a baya ga gwamnatin jiha da bin duk hanyoyin da suka dace, tare da fatar magance su.

Insha Allahu ba zan taba bata musu rai ba dangane da bukatunsu.

AMINIYA


Friday, 31 March 2023

Gobara Ta Barke A Gidan PDP

 


Ga dukkan alamu gobara ta sake barkewa a gidan babbar jam’iyyar adawa ta kasar nan wato PDP, wadda ta sake shiga rudu, makonni kadan da faduwarta a zaben Shugaban Kasa.

A ranar Talata da ta gabata ce, Kwamitin Zartarwar Jam’iyyar na Kasa (NWC), ya ayyana Ambasada Iliya Umar Damagum a matsayin Shugaban Riko na jam’iyar ta kasa.

Kafin nadinsa, Alhaji Iliya Damagum shi ne Mataimakin Shugaban Jam’iyyar PDP na kasa Shiyyar Arewa.

Kakakin Jam’iyyar PDP, Debo Ologunagba ne ya bayyana nada Damagun a ranar Talata a wani taron manema labarai a Abuja.

A sanarwar da PDP ta fitar, ta ce ya zame mata dole ta yi biyayya ga umarnin wata kotu da ta bukaci Shugaban Jam’iyyar na Kasa Dokta Ayu Iyorchia ya daina bayyana kansa a matsayin shugaban jam’iyyar har zuwa lokacin da za ta yanke hukunci kan kararsa da aka kai gabanta.

Wata Babbar Kotu a Jihar Benuwai ce ta dakatar da Dokta Iyorchia Ayu daga shugabancin Jam’iyyar PDP ta Kasa.

Alkalin Kotun, Mai Shari’a W.I Kpochi ne ya bayar da umarnin a ranar Litinin bayan sauraron kunshin karar da aka shigar Mai lamba MHC/85/2023.

Tun a ranar Juma’ar da gabata Jam’iyyar PDP ta ce ta dakatar da Shugabanta na Kasa, Iyorchia Ayu bisa zarginsa da wasu ayyuka na cin amanar jam’iyyar.


Shugabannin jam’iyyar a matakin gundumarsa da ke Karamar Hukumar Gboko, a Jihar Benuwe ne suka dauki matakin.

Sun ce sun dakatar da shi ne bayan kada kuri’ar rashin kwarin gwiwa kan ayyukansa.

A lokacin da ya karanta matsayar da shugabannin suka cim ma, Sakataren Jam’iyyar a Gundumar Igyorob, Mista Banger Dooyum ya ce zagonkasa da Ayu da na kusa da shi suka yi wa PDP ne ya janyo mata shan kaye a gundumar da kuma jihar baki daya a zaben Gwamnan da aka yi a jihar.

Sun kuma zargi Ayu da rashin biyan kudaden da ake karba na shekara-shekara daga ’ya’yan jam’iyyar, kamar yadda dokokinta suka tanada.

hugaban Kungiyar, Terzungwe Atser ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar, inda a ciki ya ce ba zai taba yiwuwa jagororin jam’iyyar su dauki wannan mataki ba a yanzu ba tare da an tursasa su yin hakan ba.

Yanzu aka fara rigimar —Wike

A bangaren Gwamnan Jihar Ribas, Nyesome Wike ya ce yanzu aka fara rigimar siyasa a tsakaninsa da dakataccen shugaban na PDP, Dokta Ayu.

Ya ce hankali ba zai dauka ba a ce wanda ya kasa kawo mazabarsa a zabubbukan da suka gabata ya ci gaba da jagorantar PDP a matsayin Shugabanta na kasa.

Wike ya bayyana haka ne lokacin da yake kaddamar da makarantar Okoro-nu-Odo da ke Karamar Hukumar ObioAkpor da ya sabunta.

Ya ce, Allah ne kadai Ya san dalilin da Ayu ya kekeshe zuciyarsa ya ki sauka daga mukaminsa a lokacin da Gwamnoni 5 da ake kira G5 suka bukaci hakan bayan Atiku Abubakar ya zama dan takarar Shugaban Kasa a PDP.

Gwamna Wike ya ce da a ce lokacin da suka bukaci haka, Dokta Ayu ya amince ya sauka, da irin su da suka yi kokarin ganin an mayar da mulki Kudu sun yi amfani da wannan wajen samun sulhu, wanda a cewarsa watakila da hakan ya sa Jam’iyyar PDP ta samu nasara.

“Ku wadanda kuke cewa kun dakatar da Ayu, ba ku ma ga komai ba.

“Ayu, yanzu aka fara rigimar nan. Wadanda suke kusa da shi su fada masa cewa yanzu aka fara,” in ji Wike.

Duk da cewa ba yanzu aka fara yunkurin cire Ayu daga Shugaban PDP na Kasa ba, wannan karon lamarin ya yi karfi matuka domin a cikin shugabannin jam’iyyar da masu ruwa-da-tsaki an samu rabuwar kai kan cire shi.

Aminiya ta samu labarin cewa an fara yunkurin ganin bayansa ne kwanaki kadan bayan zaben Shugaban Kasa, inda Jam’iyyar PDP ta sha kaye a hannun Jam’iyyar APC, rashin nasarar da wasu suka alakanta da kin amincewa ya sauka daga mukaminsa.

Aminiya ta ruwaito yadda hayaki ya fara tashi a jam’iyyar bayan Atiku Abubakar ya doke Gwamna Wike na Ribas a zaben fid-da-gwan na takarar Shugaban Kasa.

Gwamna Wike da wasu gwamnoni hudu sun ware, inda suka kafa Kungiyar G5, wadda daga cikin bukatunta akwai batun cire Ayu a matsayin shugaban jam’iyyar.

A cewarsu, ba zai yiwu ba dan takarar Shugaban Kasa da Shugaban Jam’iyya su fito daga yanki daya, wanda hakan ya sa suka bukaci Ayu ya sauka, a musanya shi da wani daga Kudu.

Hakan ya sa PDP ta shiga zaben Shugaban Kasa ba tare da gwamnonin biyar tare da ita ba, ciki har da Wikem, Gwamnan Jihar Ribas wadda take kan gaba wajen ba PDP kuri’u a zabubbukan baya.

Aminiya ta samu labarin cewa wannan yunkurin ya kara zafi ne kasancewar shugaban ya kasa hada kan jam’iyyar kafin zabe da kuma gazawarsa wajen kawo wa PDP jiharsa a zaben Shugaban Kasa da na gwamnoni, duk da cewa ba sa ga maciji da Gwamnan jiharsa ta Binuwai daya daga cikin gwamnonin G5.

Wasu abubuwan da suka kara ta’azzara rikicin shi ne batun dakatar da wasu jiga-jigan Jam’iyyar PDP da suka hada da tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Anyim Pius Anyim da tsohon Gwamnan Jihar Ekiti, Ayo Fayose da tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Ibrahim Shema kuma ta bukaci Kwamitin Ladabtarwa na Jam’iyyar da ya binciki Gwamna Ortom na Binuwai.

Jim kadan bayan dakatar da Shema ne ya fitar da sanarwa, inda a ciki ya bukaci ko dai a janye dakatarwa, ko ta zama takardar sallamarsa daga jam’iyyar, domin a cewarsa ba zai yiwu a dakatar da shi ba, inda kuma aka ce dole za a dakatar da shi, to zai bar jam’iyyar.

Daga cikin wadanda suke gaba-gaba wajen ganin an cire Ayu, akwai gwamnonin G5, wato Gwamna Nyesom Wike na Ribas da Samuel Ortom na Binuwei da Seyi Makinde na Oyo da Okezie Ikpeazu na Abiya da Ifeanyi Ugwuanyi na Enugu.

Akwai kuma wasu jigajigan jam’iyyar, ciki har da tsofaffin gwamnoni da suka hada da Ibrahim Shema da Cif Bode George da Ayo Fayose da sauransu.

Haka a cikin jagororin jam’iyyar, Aminiya ta samu labarin cewa an samu rarrabuwar kai a tsakaninsu, inda wasu suka amince a cire shi, wasu kuma suke tare da shi.

Akwai bayanan da suke cewa mai yiwuwa Dokta Ayu ya kalubalanci dakatar da shi da Kwamitin NWC ya yi a kotu, lamarin da ake jin zai kara rura wutar rikicin da ke cin jam’iyyar.

AMINIYA

Gwamnatin Kano Ta Yi Kira Ga Abba Kabir Yusuf Da Ya Jira A Rantsar Da Shi Sannan Ya Fara Bayar Da Umarni

Gwamnatin jihar Kano ta yi kira ga Injiniya Abba Kabir Yusuf da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta ayyana a matsayin zababben gwamna da ya yi hakuri tare da daina fitar da sanarwa a hukumance ta hanyar ba da shawara ga jama’a domin kada a haifar da rudani da bai kamata ba a jihar.
 
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Malam Muhammad Garba ya fitar a ranar Juma’a a matsayin martani ga umurnin da ofishin zababben gwamnan ya fitar, inda ya gargadi mutane, kungiyoyi da kungiyoyi da suke gudanar da gine-gine a wuraren taruwar jama’a da su kiyaye. .

Ya ce matakin da zababben gwamnan ya dauka ya kai ga yin tsalle-tsalle ta hanyar bayar da umarni kan lamarin da ya shafi manufofin gwamnati yayin da mai ci bai cika cika wa'adinsa ba.

Malam Garba ya kuma bayyana cewa, dangane da batun rabon mukamai kamar yadda kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya ya tanada, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya ci gaba da zama gwamna mai ikon zartarwa har zuwa ranar 29 ga watan Mayu kuma yana da hakkin gudanar da ayyukansa a maslahar jama'a ko a jajibirin fitowar sa.

“Har sai ya zama gwamna a ranar 29 ga Mayu, ya ci gaba da zama zababben gwamna kuma ba shi da ikon gwamna. Abin da kawai zai iya yi shi ne ya mayar da wasu ayyukan da magabata ya yi a lokacin da ya hau kan karagar mulki idan akwai kwararan dalilai na yin hakan. Sanarwar ta kara da cewa, babu wani zababben gwamnan da yake da ikon da kundin tsarin mulki ko doka ya ba shi na sanin alkiblar jihar har sai an rantsar da shi.

Kwamishinan ya bayyana cewa gwamnonin jihohi suna da iko da yawa wajen rabon filayen don haka kowace gwamnati ta yi irin wannan aiki ciki har da gwamnatin da ta shude wacce zababben gwamnan ya yi aiki.

Ya kuma bayyana cewa bisa ga bayanan da ake da su, gwamnatin da ta shude ta yi rabon filayen a wasu wuraren taruwar jama’a da zababben gwamnan ya ambata da suka hada da katangar birnin, tare da raba fili daga Kofar Nassarawa zuwa Kofar Mata; shaguna a filin Sallar Idi na kofar Mata da ke fuskantar gidan sinimar Orion da kuma daga Kofar Mata zuwa ‘Yan yashi daura da filin Idi da kuma daga Kofar Kabuga zuwa Kofar Famfo da ke fuskantar tsohon Campus na Jami’ar Bayero.

Malam Garba ya bayyana cewa shawarwarin da zababben gwamnan ya bayar ya haifar da tashin hankali a jihar inda ya shawarce shi da ya hakura da hakan domin gudun kawo rudani.

Ya kuma yi kira ga daidaikun mutane da kungiyoyi da suka mallaki fili bayan bin ka’idoji da tsare-tsare da kada a yi barazana da umarnin.


Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki

Zababben Gwamnan Jihar Kano Ya Sanar Da Kwamitin Karbar Mulki

…… Dr. Baffa Bichi, Abdullahi Musa ya nada a matsayin Shugaba da Sakatare

Bayan gabatar da takardar shaidar cin zabe da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta gabatar, zababben gwamnan jihar Kano Engr. Abba Kabir Yusuf (Abba Gida Gida) ya kaddamar da kwamitin sa na mika mulki a shekarar 2023.

A wata sanarwa da Sanusi Bature Dawakin Tofa, babban sakataren yada labarai na zababben gwamnan ya fitar, tsohon babban sakataren hukumar kula da manyan makarantu (TETFUND)  dan takarar Sanatan Kano ta Arewa a NNPP Dr. Abdullahi Baffa Bichi ya bayyana a matsayin shugaba na kwamitin mika mulki na Gwamna (GTC), yayin da babban sakataren dindindin, Abdullahi Musa mai ritaya a matsayin sakatare.

Kwamitin rikon kwarya zai gudanar da ayyukan mika mulki cikin tsari daga gwamnatin Ganduje mai barin gado zuwa gwamnatin Abba Gida Gida mai jiran gado.

Mai girma Gwamnan Jihar Kano mai jiran gado zai kaddamar da kwamitin a ranar Asabar 1 ga Afrilu, 2023 da karfe 2:00 na rana. Jadawalin Da ke ƙasa akwai cikakken jerin membobin Babban Kwamiti, yayin da za a sanar da ƙananan kwamitoci a sassa daban-daban da ƙananan sassa nan gaba.

Thursday, 30 March 2023

Zababben Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf, Ya Yi Kira Da A Dakatar Da Duk Wasu Gine-gine Da Ake Yi A Marantu, Makabarta da Kasuwanni

Zababben Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya bayar da umarnin a bayar da wannan Shawara ga Jama’a da duk daidaikun mutane, kungiyoyi da sauran kungiyoyi da suke ci gaba da gine-gine a wuraren taruwar jama’a cikin wata sanarwa da babban daraktan yada labaransa, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu kamar kamar:

a. Ana shawartar ku da ku daina aikin gine-gine a filayen jama'a a ciki da kewaye: Dukkanin Makarantu na Jiha, duk wuraren addini da al'adu na jihar, duk asibitocin jihar, duk makabarta a cikin jihar, da kuma jikin Badalar Kano;

b. Ana kuma shawarce ku da ku daina rushewa, da kuma gina duk wasu gine-ginen gwamnati na gwamnati da jama'ar jihar Kano;

c. An bayar da wannan Shawarar ne domin amfanin jama'a, daga yau Alhamis 30 ga Maris, 2023 har zuwa sanarwa ta gaba. Duk wani wanda ya sabawa haka  yana yin haka duk abun da ya faru shi ya jawo



Bashin Da Ake Bin Najeriya Ya Karu Zuwa Naira Tiriliyan 46.25 - DMO

Ofishin Kula da Basussuka na Kasa (DMO) ya ce bashin da ake bin Najeriya ya karu zuwa Naira tiriliyan 46.25 a watan Disamban 2022.

A wata sanarwa a ranar Alhamis, DMO ya ce an samu karin sama da Naira tiriliyan bakwai daga abin da kasar ta mallaka a shekarar 2021.

Kano: Ba zan rika yi wa gwamnatin Abba katsa-landan ba – Kwankwaso
Masari: Tinubu na bukatar addu’a
“Jimillar Bashin Jama’a wanda ya kunshi bashin cikin gida da na kasashen waje na Gwamnatin Tarayya da kananan hukumomi daga (Gwamnatin Jihohi 36 da Babban Birnin Tarayya), ya kai Naira Tiriliyan 46.25 ko kuma dala biliyan $103.1, kwatankwacin adadin ranar 31 ga watan Disamba, 2021, na Naira tiriliyan 39.5 wanda ya yi daidai dad ala biliyan $95.77.

“Ta fuskar hada-hadakuwa, jimillar bashin cikin gida ya kai Naira tiriliyan 27.55 daidai da dala biliyan $61.42, yayin da jimillar bashin waje ya kai Naira tiriliyan 18.7t daidai da dala biliyan $41.6.


Ofishin ya bayyana cewa dalilan da suka sa aka kara samun yawan bashin gwamnati; su ne sabbin rancen da Gwamnatin Tarayya da na kananan hukumomi suka yi, na farko, don samar da gibin kasafin kudi da aiwatar da ayyuka.

“Bayar da bayanan lamuni da gwamnati ta yi don daidaita wasu lamura shi ma ya ba da gudunmawa wajen karuwa bashin.”

Sai dai ta ce kokarin da gwamnati ke ci gaba da yi na kara samun kudaden shiga daga albarkatun mai da wadanda ba na mai ba ta hanyar tsare-tsare irin su Dokar Kudi da kuma dabarun tattara kudaden shiga na iya tallafawa dorewar bashi.
AMINIYA 

Zababben Gwamnan Kano Ya Nada Tsohon Dan Jarida, Sanusi BatureBabban Sakataren Yada Labaransa

Zababben Gwamnan Jihar Kano H.E. Engr. Abba Kabir Yusuf ya bayyana Sunusi Bature Dawakin Tofa a matsayin babban sakataren yada labaran sa na lokacin mika mulki.

A cikin wata takarda mai dauke da sa hannun shugaban kwamitin mika mulki na gwamna a madadin gwamnan jihar, mai girma gwamna ya bayyana nadin na Bature a matsayin wanda ya dace da shi a bisa cancantarsa ​​da rikon amana da jajircewarsa da kwazonsa da ya nuna tun 2019.

Sunusi kwararre ne a fannin yada labarai da hulda da jama’a sadarwar ci gaba da Æ™wararrun masu ruwa da tsaki tare da gogewar shekaru 19 na aiki a cikin ci gaban Æ™asa da Æ™asa, kamfanoni masu zaman kansu da kuma Media a Najeriya.

Shi ne wanda ya lashe lambar yabo ta ilimi ta Cambridge kan aikin jarida a 2008, Bature ya yi aiki a wurare daban-daban a kungiyoyi daban-daban na kasa da kasa da na kasashen biyu kamar Ofishin Harkokin Waje da Kasuwanci na Burtaniya (FCDO), Hukumar Ci Gaban Cikin Gida ta Amurka (FCDO). USAID), Bill da Melinda Gates Foundation, Save the Children International, Discovery Learning Alliance da kuma Gidauniyar Rockefeller.

Ya rike mukamai da dama wadanda suka hada da General Manager Corporate Services a Dantata Foods and Allied Products Limited (DFAP), Director Stakeholder Engagement at YieldWise Project, Country Program Manager at Girl Rising (ENGAGE) Project wanda Gwamnatin Amurka ta ba da tallafi, Mai Gudanar da Ayyukan Jiha na MNCH Campaign. Ayyukan BMGF, Mataimakin Darakta Ayyuka a Ƙwararrun Ƙwararrun Ƙwararru, Jami'in Shirye-shiryen Jiha, Ƙwararrun Siyasa da Ci Gaban Watsa Labarai, Sadarwa da Ƙwararrun Gudanar da Ilimi a tsakanin sauran mukamai.

Sanusi ya kammala digirinsa na farko (B.A. Hons.) a Mass Communication a Jami’ar Maiduguri, ya yi Diploma na kasa kan Mass Communication a Kaduna Polytechnic, Diploma Higher National Diploma (HND) da Difloma a fannin Ilimin Kiwon Lafiyar Jama’a da Ci gaba.

Ya kuma yi digiri na biyu . a cikin Ayyukan zamantakewa tare da ƙwarewa a Ci gaban Al'umma daga Jami'ar Fasaha ta Ladoke Akintola, (LAUTECH) Ogbomosho, Jihar Oyo da kuma wani digiri na biyu a Harkokin Jama'a (MPR) daga Jami'ar Bayero mai daraja, Kano, Nigeria. Ya shiga cikin shirin MSc akan Gudanar da Ayyuka a Kwalejin Robert Kennedy, Zurich, Switzerland.

Har zuwa lokacin da aka nada shi, Sunusi Bature ya rike mukamin mataimakin shugaban kasa a Najeriya a wani kamfani mai suna Kingston Organic PLC da ke Burtaniya.

Wednesday, 29 March 2023

Yanzu-Yanzu: Nasiru Gawuna Ya Taya Abba Gida-gida Murnar Lashe zaɓen Gwamnan Kano

Mataimakin Gwamnan Jihar Kano Kuma wanda ya yiwa jam’iyyar APC takarar gwamnan jihar kano a jam’iyyar APC Dr. Nasiru Yusuf Gawuna ya ce ya karÉ“i Kaddarar faÉ—uwa zaÉ“e tare da taya Abba Kabiru Yusuf Murnar lashe zaÉ“en gwamnan Kano.

Nasiru Gawuna ya bayyana hakan ne cikin wani sakon murya da yayi bayani na tsawon mintuna biyu, wanda Sakataren yada labaran sa Hassan Musa Fagge ya aikowa kadaura24.


” Mun tsammaci Hukumar Zabe INEC zata duba koken da mukai mata na samun kura-kurai a sakamakon zaben da ya gudana, amma a yau 29 ga watan maris ta sake tabbatar da matsayar ta ta hanyar mikawa Abba Kabiru Yusuf Shaidar lashe zabe , don haka mun dauki wannan a matsayin kaddara”. Inji Gawuna


 
Yace dama ya fada a baya cewa zai karÉ“i Kaddara idan ya fadi zaben don haka yayi kira ga magoya bayan sa da dukkanin al’ummar jihar kano da zu baiwa sabon zaÉ“aɓɓen gwamnan hadin kai don ya gudanar da mulkin sa cikin kwanciyar hankali da lumana.

 
Mataimakin Gwamnan ya kuma yi addu’ar Allah ya kamawa Sabon zababben gwamnan, sannan yayin addu’ar Allah ya bashi ikon yiwa al’ummar jihar kano adalci a Shugabanci sa.
KADAURA24 


Tuesday, 28 March 2023

Zababben Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf na ya al'ummar Kano domin su Karbar Shaidar Cin Zabensa

Zababben Gwamnan Jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf, wanda aka fi sani da Abba Gida Gida yana gayyatar dumbin magoya bayansa, mambobin jam'iyyar NNPP da kuma manyan masu ruwa da tsaki, zuwa gabatar da takardar shaidar cin zabe ga dukkan 'yan takarar da suka ci zabe a ranar Asabar 18 ga wata.

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) a Kano ta shirya ranar Laraba 29 ga Maris, 2023 da karfe 10 na safe a sakatariyar INEC don bayar da shaidar cin zabe ga zababben gwamna da mataimakinsa da ‘yan majalisar jiha.

Kakakin zababben gwamnan jihar Kano, Sanusi Bature Dawakin-Tofa, a wata sanarwa a ranar Talata ya ce za a gudanar da taron ne a dakin taro na INEC da karfe 10:00 na safe.

Ya kuma bukaci magoya bayan jam’iyyar NNPP da duk wadanda aka gayyata, wadanda suka shahara da son zaman lafiya da bin doka da oda, da su rika gudanar da harkokinsu cikin tsari a lokacin bikin da kuma bayan bikin, tare da yi wa kowa fatan alheri.

SABATURE

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

Head of Service Urges Civil Servants to Uphold Ethical Conduct

The Head of Service, Kano State, has called on civil servants to strictly adhere to the Civil Service ethical code and show grea...