Masu Niyyar Zuwa Aikin Hajji Mai Zuwa, Zasu Ga Tagomashi Daga Gwamnatin Abba Gida - Zulaiha Yusuf Aji

Maitamakawa gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf a kan kafafen yada labarai na rediyo da talbinjin Hajiya Zulaihat Yusuf Aji, ta ce gwamnatin jihar Kano duk da sabuwa ce amma ta yi kokari mutuka, idan ka duba gwamnatin ce da ta shigo daf da za fara dibar alhazai wanda tuni wasu jihohin sun fara jigilar maniyatan, amma abun da zai baka mamaki shi ne tun a Madina a ka fara bawa alhazan Kano abinci sau uku a rana baya ga kawo motoci a debe su zuwa guraren ziyara a Madina sannan a ka kuma dauko su zuwa Mak
ka.

"Mun zo Makkah kuma mun je Mina, zaman Mina alhamdulillah wakiliyar sashin Hausa ta muryar Amuruka Baraka ta hira da ni kan matsalolin takari mazauna kasar Saudiya ina ganin akwai matakin da za a dauka

"Tun a jirgin farko da za su fara tashi mai girma gwamna ya zo ya yi musu sallama yayi musu bakwana ya kuma ba su hakuri, duk abun da su ka gani a Mina su yi hakuri ba wannan gwamnatin ce ta tsara musu ba. Duk alhaji da ya wannan shekarar a shekara mai zuwa idan ya zo sha mamaki."


Da wakilcin mankyarmu ya tambaye ta cewa, ba ta ganin shi aikin gwamnati dorawa a ke yi a inda ta baya ta tsaya kuma wannan kamar gazawar sabon shugaban hukumar jindadin alhaza. 

"A a in ka duba ya cancanci ya yabawa sabon shugaban hukumar alhazai ta jihar Kano ta yadda yanayin abun ya zo a kurace a kuma nada shi shugabamcin a kurace to abun ajinjinawa Hon Laminu Rabiu Dambaffa ne kwarai da gaske sun yi kokari shi da mataimakansa saboda ba karamin jajirtaccen mutum za ba bawa wannan matsayin a wannan dan kankanen lokacin a cimma wannan biyan bukatar 

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki