Kungiyar Kwadago Ta Kasa Za Ta Fara Gudanar Da Yajin Aiki

Kungiyar Kwadago ta Najeriya NLC, ta baiwa gwamnatin tarayya wa’adin kwanaki bakwai da ta sauya duk wasu manufofin da ake ganin na yaki da talakawa, ciki har da karin farashin man fetur da aka yi a baya-bayan nan, ko kuma ta fuskanci yajin aikin gama gari daga ranar 2 ga watan Agusta.

Kungiyar kwadago ta NLC ta umurci dukkanin kungiyoyin ta da kuma majalisun jihohi da su gaggauta fara shirin daukar ma’aikata da sauran ‘yan Najeriya da suka hada da kungiyoyin farar hula don gudanar da yajin aikin da za a dade da gudanar da zanga-zanga idan har gwamnati ta gaza biyan bukatunta.

Jaridar Nigerian Tracker ta rawaito cewa wannan na daya daga cikin shawarar da aka cimma a taron kwamitin tsakiya na NLC, CWC, wanda aka gudanar a ranar Talata, 25 ga watan Yuli, a gidan ma’aikata na Abuja.

Cikakken labarin zai zo muku nan gaba 

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki