Posts

Showing posts from February, 2024

'Yan Bindiga Sun Sace Mutum Talatin Lokacin Sallah A Zamfara

Image
Wani ganau ya ce ’yan bindigar sun mamaye masallacin ne da misalin karfe 5 na Asuba, a lokacin da ake shirin fara salla. Garba ya ce, “Za mu fara sallar asuba, kwatsam sai ’yan bindiga suka shigo masallaci suka umarci kowa ya fito ya bi su. “Kowa ya yi kokarin guduwa domin tsira amma suka tare ko’ina suka gargade mu cewa za su kashe duk wanda ya yi yunkurin guduwa. “Na samu na iya tsalle daga tagar kuma da sauri na shiga wani kango da ke kusa da masallacin na boye kaina,” in ji shi. Shaidan ya bayyana cewa ’yan bindigar sun bar baburansu a nesa da masallacin don kada a lura da motsinsu. Ya kara da cewa, “Daga baya sun tafi da mutanen zuwa inda baburansu suke, suka tafi da su.” A cewarsa, adadin mutanen da aka sace a masallacin zai iya wuce 30. Ya kara da cewa “masallacin ya cika a lokacin da suka kai hari kuma kadan ne daga cikin mu suka samu tsira.” Daya daga cikin shugabannin yankin wanda ya nemi a sakaya sunansa ya ce jami’an tsaro na ci gaba da bin diddigin ’yan bindiga

Sababbin Shugabannin NAHCON Sun Kama Aikinsu Bayan Da Mataimakin Shugaban Kasa Ya Kaddamar Da Su

Image
A ranar Laraba ne Hukumar kula da aikin Haji ta kasa ta shaida wani muhimmin lamari, yayin da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya kaddamar da shugabancinta a karo na biyar karkashin jagorancin Malam Jalal Ahmed Arabi Taron kaddamarwar ya faru ne a ofishin mataimakin shugaban kasar, inda bayan nan ne shugabannin suka zarce zuwa hukumar A sanarwar da mataimakiyar daraktar harkokin hulda da jama'a da dab'i ta hukumar, Fatima Sanda Usara ta sanyawa hannu, tace a yayin gudanar da taro shugabannin hukumar ta NAHCON, shugaban hukumar, Malam Jalal Arabi, yayi maraba da dukkanin wakilaninda ya bayyana kwarin gwiwarsa ga cancantarsu, inda ya kuma basu tabbacin samun hakan daga bangaren ma'aikatan hukumar kamar yadda shi ma ya samu yayin da ya kama aiki a watanni hudun da suka gabata. Daga nan sai yayi kira ga ma'aikatan hukumar su bayar da makamancin hadin kan sababbin shugabannin nasu don cimma manufar hukumar Sababbin shugabannin da aka nada sun

Mataimakin Shugaban Kasa Ya Kaddamar Da Sababbin Shugabannin NAHCON

Image
Mataimakin shugaban kasa, Sanata Kashim Shettima ya kaddamar da sababbin Jami'an hukumar alhazai ta kasa (NAHCON) tare da yin kira ga da su bullo da sabbin abubuwa a harkokin aikin hajji a Najeriya.  A sanarwar da mai taimakawa Mataimakin Shugaban kasar kan harkokin yada labarai  Stanley Nkwocha ya sanyawa hannu, yace d a yake jawabi yayin kaddamar da sababbin 'yan hukumar a fadar shugaban kasa da ke Abuja ranar Laraba, mataimakin shugaban kasar ya bukaci mambobin su hada kai tare da kawo sabbin ra’ayoyi kan ayyukan hukumar. A cewar Sanata Shettima, yin aiki a hukumar NAHCON na da matukar muhimmanci ganin cewa “Hajji na daya daga cikin rukunan Musulunci guda biyar”. “A gare ku, bayan nadaku da aka yi, abu ne mai nasara domin idan kun yi wa alhazai hidima da kyau, Allah Ta’ala zai biya ku a ranar lahira. Don haka, aikinku ya fi kusanci da na addini fiye da aikin gudanarwa,” in ji Shettima.  Da yake karin haske game da batun kafa sabuwar hukumar da aikin d

Jinkirin Mika Fasfon Maniyyata Na Kawo Cikas Ga Aikin Yin Bizar Aikin Hajji - Laminu Rabi'u

Image
Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano, Alhaji Laminu Rabi’u Danbappa, ya bayyana  jinkirin mika fasfo  ga hukumar a matsayin  babban kalubalen da ke kawo cikas wajen yin Bizar aikin Hajji ga maniyyata Yayin wata ziyara zuwa daya daga cikin cibiyoyin bitar Alhazai  da aka gudanar a karamar hukumar Doguwa a yau, Alhaji Laminu Rabi’u Danbappa ya jaddada muhimmancin bayar da fasfo a kan lokaci wajen saukaka gudanar da bizar aikin Hajji cikin sauki ga maniyyata. A cikin sanarwar da Jami'in hulda da jama'a na hukumar, Sulaiman Abdullahi Dederi ya sanyawa hannu, yace Alhaji Danbappa, wanda wakilin hukumar gudanarwa na hukumar, Malam Ismail Mangu ya wakilta, ya bayyana cewa, “jinkirin tura fasfo na kasa da kasa yana kawo cikas wajen gudanar da aikin Hajji yadda ya kamata ga maniyyatan mu, ya zama wajibi mu daidaita wannan aiki domin tabbatar da kammala aikin a kan lokaci. da kuma inganta aikin hajji gaba daya”. Malam Ismail Mangu ya kara jaddada muhimmanc

Babu hannunmu a tashin farashin kayan abinci -- Dangote

Image
Babbar Darakta a rukunin kamfanonin Dangote, Hajiya Fatima Aliko Dangote, ta bayyana cewa rukunin kamfanonin Dangote ba su da hannu a tashin farashin kayayyakin abinci da ake fuskanta a kasar nan. Daily Nigeria Hausa ta rawaito cewa wata hira da Sashen Hausa na BBC, Hajiya Fatima ta ce kamfanin ya sayar da bangaren sarrafa abinci shekaru biyar da suka gabata ga Olam Group da ke sarrafa abinci da kasuwancin noma a Najeriya. Ta ce Olam a yanzu shi ne ke samar da fulawa, taliya, semolina, kuma duk wata fulawa da ake samu a kasuwanni ba kamfanin Dangote ne ke samar da ita ba. “A cikin yarjejeniyar cinikin, an amince da cewa za su ci gaba da yin amfani da sunanmu da tambarin muwajen yin kayayyakinsu, kuma nan da shekara mai zuwa za su daina. “Mu yanzu sukari, gishiri, da kayan yaji na Dangote kawai muke samarwa. Har ila yau, muna fatan za mu fara noman shinkafa nan gaba ko kuma badi,” in ji ta. Fatima ta kara da cewa ba su ji dadin yadda farashin kayayyakin ke hawa ba kuma kamf

Yadda Dalar Amurka Ke Jefa ’Yan Nijeriya Cikin Kunci

Image
Hauhawar farashin Dalar Amurka ya biyo bayan dokar da Shugaba Tinubu na barin Naira ta kwaci kanta a kasuwa. A ranar Litinin ta makon jiya ce Uwargidan Shugaban Kasa, Sanata Remi Tinubu ta kai ziyara Jihar Kano domin kaddamar tsangayar karatun lauyanci na Jami’ar Maryam Abacha, wato MAUN. A lokacin ziyayar ce Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero ya ba wa Remi Tinubu sako ta sanar da mijinta cewa, al’ummar Nijeriyar na cikin halin kaka-nika-yi, saboda haka ya yi abin da ya dace. Sai dai tun a farko, Uwagidan Shugaban Kasar ta yi kira ga mutanen Nijeriya da su kwantar da hankalinsu, inda ta tabbatar da cewa lallai akwai haske da nasara a gaba. Idan ba a manta ba, tun a jawabin da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi lokacin rantsuwar karbar mulki, a ranar 29 ga watan Mayu ya bayyana cire tallafin man fetur, abin da ya haifar da karin kudin man nan take daga Naira 195 zuwa 540 a kan kowace lita daya. Sannan hauhawar farashin Dalar Amurka ya biyo bayan dokar da Shugaba Tinubu na barin Nai