Hajj2024: NAHCON Ta Ja Hankalin Hukumar Kula Da Filayen Jiragen Kan Samar Da Kayayyakin Da Suka Wajaba

Hukumar Alhazai ta kasa ta hori hukumar dake lura da filayen jiragen sama ta kasa, da ta gaggauta samar da dukkanin kayayyakin da suka waja a bangare tashin alhazai da nufin gudanar da jigilar alhazan na wannan shekarar cikin nasara

A sanarwar da mataimakin Daraktan yada labarai da dab’I na hukumar , Mousa UIbandawaki ya sanyawa hannu, yace Mai rikon mukamin shugabancin hukumar, Malam Jalal Ahmed Arabi, shi ne yayi wannan kiran lokacin da wakilin hukumar na bangaren aikin Haji suka kai masa ziyarar ban girma a Abuja

Ya bayyana cewa samar da kayayyakin da suka wajaba a bangaren tashin alhazan dake fadin kasar nan zai taimaka matuka gaya wajen samun nasarar aikin jigilar alhazan

‘’Ku manyan abokan hula ne wajen gudanar da aikin Haji. Koda yake akwai wasu abubuwa da ake la’akari dasu yayin tashin alhazai kuma muna sa ran zaku sanar mana yanayin da filiyen jiragen saman da ake amfani dasu waje n tashin alhazai suke ciki’’

Ya bayyana cewa kwamitin ya kamata yay duba da lokaci domin saboda lokacin da suke da shi kadan ne wajen gudanar da aikinsu, duba da wa’adin da kasar Saudia ta bayar ga dukkanin kasashe wajen kamala shirinsu na aikin Haji da wuri

Tunda farko da yalke nasa jawabin, jagoran tawagar, wanda kuma ya kasance daraktan kula da ayyukan filin jiragen sama na hukumar, Kaftin Muktar Yusuf Muye, ya bayyana cewa hukumar ta shirin aikin shekara na Hajin 2024 tun watanni biyu da suka gabata domin samun nasarar gudanar da shi

Ya bayar da tabbacin cewa zasu kamala aikin kafin fara jigilar alhazai a dukkanin wuraren tashin alhazai dake filayen jiragen sama na fadin kasar nan

A saboda haka sai Kaftin Muye yayi kira ga NAHCON da ta ja hankalin kamfanoni masu zaman kansu dake jigilar alhazai dasu bayar da hadin kai ga tsarin aikin jigilar alhazansu ta bangaren tashi zuwa kasa da kasa a maimakon banagren tashin alhazai domin hakan na hana hukumar samun kudaden shiga masu muhimmanci wanda ya kamata su samu don samar da muhimman kayan inganta rayuwa a filayen jiragen

Daga nan sai ya bawa hukumar tabbacin aniyarsu wajen gudanar da aikin yadda ya kamata don alhazan Najeriya su samu damar guanar da aikin Hajin 2024 ba tare da wata matsala ba

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki