Posts

Hajj2023 - Hukumar Alhazai Ta Kano Za Ta Fara Aikin Gwajin Juna Biyu Ga Maniyyata Mata

Image
Hukumar kula Jin dadin alhazai ta Jihar Kano, na sanar da Maniyyata Mata na Jihar Kano cewa za'a fara Gwajin Juna-biyu wato ( Scanning ) ga Maniyyata Mata  Matan da za a fara dasu a gobe Lahadi 21 ga watan Mayu 2023, kamar yadda sanarwar da Mataimakiyar Daraktar harkokin Ilmantarwa da hulda da jama’a ta hukumar Hajiya Hadiza Abbas Sanusi ta rabawa manema labarai, sun hada da na kananan hukumomin Takai, Sumaila, Garko, Albasu, Tudun wada, Bebeji, Doguwa da Karamar Hukumar Garun Malan Haka kuma sanarwar ta kara da cewa za a gudanar da aikin a Sansanin alhazai na Jihar Kano wato Hajjcamp da misalin karfe Tara na safe

Shugaban EFCC Ya Nemi Cin Hancin Dala Miliyan Biyu Daga Wajena - 1 Gwamna Matawalle

Image
Gwamnan jihar zamfara, Bello Matawalle ya zargi shugaban hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, Abdulrasheed Bawa da neman cin hancin dala miliyan biyu daga gare shi. Matawalle ya yi wannan zargin ne a wata hira da BBC Hausa a ranar Juma’a, a daidai lokacin da ake ci gaba da takun saka tsakanin gwamnan da hukumar yaki da cin hanci da rashawa. Idan za a iya tunawa, a wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba, Matawalle ya yi kira ga Bawa ya yi murabus, yana mai cewa yana da tambayoyi da zai amsa kan cin hanci da rashawa. Sai dai Shugaban na EFCC ya amsa cewa ba shi da wani abin boyewa yayin da ya bukaci Matawalle da ya kai karar hukumomin da suka dace idan yana da wata shaida a kansa. Duk da haka, da yake magana yayin hirar, Matawalle ya dage cewa ba za a iya amincewa da Bawa ba. Ya ce, “Ba wai kawai a rika zargin gwamnoni ba ne. Ba gwamnoni kadai ke da baitulmali ba, gwamnatin tarayya ma tana da. Me shugaban EFCC yake yi musu? Kamar yadda yake ikirari yana

Yanzu-Yanzu : Kotu Ta Soke Zaben Zababben Gwaman Jam'iyar LP Alex Otti

Image
Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kano, ta soke zaben zababben gwamnan jihar Abia, Dr Alex Otti da daukacin ‘yan takarar jam’iyyar Labour a jihohin Abia da Kano. Kotun da Mai shari’a M N Yunusa ke jagoranta ta ce fitowar tasu bai bi ka’idojin dokar zabe ta 2022 ba. An mika kwafin hukuncin da kotun ta yanke ga manema labarai a ranar Juma’a. Kotun da ta shigar da kara mai lamba FHC/KN/CS/107/2023 da Mista Ibrahim Haruna Ibrahim ya shigar kan jam’iyyar Labour da kuma Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC, ta ce jam’iyyar Labour ta gaza mika rajistar zama mambobinta ga INEC a cikin Kwanaki 30 kafin zabukan firamarensu ya sa tsarin ya zama mara inganci. “Jam’iyyar da ba ta bi tanade-tanaden dokar zabe ba, ba za a ce tana da dan takara a zabe kuma ba za a iya bayyana ta a matsayin wadda ta lashe zabe ba; saboda haka, kuri’un da aka baiwa wanda ake kara na 1, kuri’a ce ta bata,” inji alkalin. Idan dai za a iya tunawa INEC ta bayyana Otti na jam’iyyar Labour a matsayin

Yajin aikin likitocin Najeriya ya jefa majinyata a halin kunci

Image
Tarin asibitoci a sassan Najeriya sun fada halin garari saboda karancin likitocin da ke duba marasa lafiya sakamakon yajin aikin gargadin da kungiyar likitoci masu neman kwarewa ta NARD ke yi kasar, inda bayanai ke nuna cewa tuni majinyatan da ke bukatar kulawar gaggawa suka sauya akalar duba lafiyarsu zuwa asibitoci masu zaman kansu sakamakon cunkoson da ake gani a asibitocin gwamnati. A larabar da ta gabata ne mambobin kungiyar ta NARD suka tsunduma yajin aikin a wani yunkuri na nuna bacin ransu game da rashin cika musu alkawuran da ke tsakaninsu da gwamnati ciki har da karin albashi da akalla kasha 200. Sai kuma yunkurinsu na kalubalantar kudirin dokar da ke gaban Majalisar kasar da ke shirin kange daga fita ketare don yin aiki har sai bayan sun yi aikin shekaru 5 a cikin Najeriya. Haka zalika kungiyar likitocin na bukatar gwamnatin Najeriyar ta biya mambobinta bashin kudaden albashin da suke binta tun shekarar 2015 baya daukar tarin ma’aikatan bangaren lafiya saboda kar

Ba Ni Da Gida A Kasar Waje - Buhari

Image
Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya ce ba shi da gida a wajen Najeriya. Ya bayyana haka ne a lokacin da yake karbar wasikar girmamawa daga jakadan Birtaniya a Najeriya, Richard Hugh Montgomery da takwaransa na Sri Lanka Velupillai Kananathan a fadar shugaban kasa a ranar Alhamis. Buhari ya ce “A daya daga cikin ganawarmu da Sarki Charles III, ya tambaye ni ko ina da gida a Ingila, amma na shaida masa cewar ba ni da gida a wajen Najeriya.” Ya kara da cewa, an shafe shekaru da yawa ana musayar al’adu ta hanyar ilimi da horarwa tare da Birtaniya, inda ya nuna cewa ya samu horon soji a makarantar Mons Officer Cadet da ke Aldershot a Ingila 1962 zuwa 1963. Buhari ya shaida wa jami’in diflomasiyyar Birtaniya cewa kyakkyawar fahimtar banbance-banbancen al’adu, da mutunta cibiyoyi shi ne ya share fagen yawan nasarorin da Birtaniya ta samu. Ya ce jami’an diflomasiyyar da suka gabata sun kulla alaka da Sarkin Musulmi, Sarkin Kano, Shehun Borno da Sarkin Ilorin. Shugaba Buhari ya kuma

El-Rufai Zai Rushe Kamfanoni 9 Mallakar Makarfi

Image
Gwamna Nasir El-Rufai na Jihar Kaduna, ya soke lasisin mallakar kamfanoni tara na tsohon gwamnan jihar, Sanata Ahmed Muhammed Makarfi. An kuma shirya rushe kamfanoni tara mallakar tsohon gwamnan Jihar. Aminiya  ta fahimci cewa an kai sanarwar janye  hakkin mallaka ga jami’an kamfanonin da abin ya shafa. Sanarwar ta fito ne daga Daraktan kamfanin rake da ke lamba 11 a Murtala Square, Alhaji Ibrahim Makarfi wanda ya mayar da martani da cewa, “lauyoyinmu za su mayar da martani kan kwace hakkin mallakar kamfanonin”. Sai dai da yake mayar da martani kan soke hakkin mallakar a wani sakon da ya aike wa Sanata Makarfi, ya tabbatar da samun wasikun soke kamfanonin har guda tara. Ya ce, “Akwai babban batu. Muna bukatar ganawa da Ustaz Yunus (SAN) domin mu garzaya kotu don dakatar da gwamnatin jiha; kawai sun aiko mana da takardun soke mallaka guda tara”. Daga cikin kadarorin da abin ya shafa sun hada da filaye guda biyar a Mogadishu, filaye uku a kan titin Kwato, da fili daya a Doka.

Hajj2023 : Hukumar NAHCON Ta Kaddamar Da Tawagar 'Yan Jaridu

Image
Shugaban Hukumar Alhazai ta Najeriya, NAHCON, Alhaji Zikrullah Kunle Hassan, ya kaddamar da tawagar kafafen yada labarai na kasa domin gudanar da aikin Hajji na shekarar 2023 a kasar Saudiyya. Taron ya gudana ne a ofishin da ke Abuja ranar Alhamis. Hassan ya jaddada mahimmancin bin ka'idojin Æ™wararru, gami da daidaito a aikin jarida. Ya taya ‘yan tawagar murna da aka zabo su, ya kuma bukace su da su dauki kansu a matsayin abokan hadin gwiwa da NAHCON wajen gudanar da aikin Hajji ba tare da wata matsala ba. Shugaban hukumar ya bayar da tabbacin cewa za a kwashe dukkan maniyyatan da suka yi rajista a jirgi a kan lokaci, inda ya ce jami’an NAHCON za su tafi kasar Saudiyya ranar 21 ga watan Mayu domin yin shirye-shiryen da suka dace. Ya nanata kudurin hukumar na tabbatar da cewa alhazai sun samu kimar kudinsu kuma an dauke su cikin gaggawa. Da yake magana kan da rawar da kafafen yada labarai ke takawa, shugaban NAHCON ya yi kira ga kungiyar kafafen yada labarai

Labari da dumiduminsa : Tinibu Zai Zo Kano Domin Bude Ayyuka - Ganduje

Image
Gwamnan jihar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana cewa ana sa ran zaÉ“aÉ“É“en shugaban Æ™asa Bola Ahmad Tinubu zai zo jihar kano domin bude wasu aiyuka da gwamnatinsa gudanar a nan kano.   ” A yayin da muka cigaba da bude wasu daga cikin aiyukan raya kasa da gwamnatinmu ta yi a kwarya birnin kano da kewaye, Muna sa rana ZaÉ“aÉ“É“en Shugaban kasa Asiwaju Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano domin kaddamar da sabuwar gadar da muka Samar a kofar mata zuwa Ibrahim Taiwo Road”. Kadaura24 ta rawaito Ganduje ya bayyana hakan ne yayin da yake jagorantar taron majalisar zartarwar ta jihar kano na wannan makon a gidan gwamnatin jihar kano. Ganduje yace ya bude aiyuka Masu tarin yawa Kuma zai cigaba da bude aiyukan don raya kasa da gwamnatinsa ta gudanar. Ganduje dai ya na bude aiyukan da ya gudanar ne a wani bangare na bankwana ga al’ummar jihar kano sakamakon karewar wa’adin gwamnatin sa a ranar 29 ga watan mayu.

An faɗa mana ƙarasa ayyukan da wasu suka faro babbar nasara ce - Zaɓaɓɓun gwamnoni

Image
  An faÉ—a wa zaÉ“aÉ“É“un gwamnonin da za a rantsar ranar 29 ga watan Mayu a Najeriya, cewa a cikin nasarar shugabanci, akwai Æ™arasa ayyukan da magabatansu, suka faro. Matakin zai taimaka wajen tabbatar ci gaban Æ™asa da alkinta dukiyar al'umma da rage kashe kuÉ—i wajen gudanar da harkokin mulki a matakan jihohi. Wannan jan hankalin, na cikin É—umbin bayanai da shawarwari da aka gabatar wa zaÉ“aÉ“É“un gwamnonin Najeriya, yayin wani taron sanin makamar aiki da aka shirya musu a babban birnin Æ™asar, Abuja. Manufar taron na kwana uku, ita ce shirya gwamnonin masu jiran gado da dabaru da hikimomin shugabanci kafin a rantsar da su nan da kwana 12. Ƙungiyar gwamnoni ta Najeriya ce ta shirya taron a Abuja, inda ta gayyato Æ™wararru a fannoni daban-daban game da sanin dabarun shugabanci a ciki da wajen Æ™asar domin bunÆ™asa Æ™warewar sabbin gwamnonin. Jiga-jigan 'yan siyasa kamar Simon Lalong na jihar Filato da Nasiru El-rufa'i da su Kayode Fayemi sun ja hankalin zaÉ“aÉ“É“un gwamnonin da za su hau

Abun Da Tinibu Da Kwankwaso Suka Tattauna A Kasar Waje

Image
Shugaban kasa mai jiran gado, Bola Tinubu ya yi wata ganawar sirri da dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Kwankwaso a kasar Faransa. Wata majiya mai tushe ta ce Tinubu ya yi wa Kwankwaso tayin tafiya tare da shi a sabuwar gwamnati da kuma duba yiwuwar sulhu tsakaninsa da Gwamnan Kano mai barin gado, Abdullahi Ganduje. A ranar Litinin, mako biyu kafin Tinubu ya karbi rantsuwar fara aiki, suka shafe sama da awa hudu suna ganawar sirrin da Kwankwaso a birnin Paris na kasar Faransa. Majiyarmu ta ce a yayin ganawar, Tinubu ya bukaci hadin kai domin aiki tare da Sanata Kwankwaso — wanda ya lashe kuri’un Jihar Kano a zaben 2023. Kwankwaso da shugaban kasar da ke jiran rantsarwa nan da mako biyu masu zuwa sun kuma amince za su ci gaba da tattaunawa kan wannan batu. Majiyar ta ce mai dakin Kwankwaso da zababben Sanata Abdulmumini na Jam’iyyar NNPP ne suka raka madugun Kwankwasiyya zuwa wurin ganawar. A bangaren Tinubu kuma, matarsa, Sanata Oluremi da Mataimakin