Search This Blog

Saturday, 20 May 2023

Hajj2023 - Hukumar Alhazai Ta Kano Za Ta Fara Aikin Gwajin Juna Biyu Ga Maniyyata Mata

Hukumar kula Jin dadin alhazai ta Jihar Kano, na sanar da Maniyyata Mata na Jihar Kano cewa za'a fara Gwajin Juna-biyu wato ( Scanning ) ga Maniyyata Mata 

Matan da za a fara dasu a gobe Lahadi 21 ga watan Mayu 2023, kamar yadda sanarwar da Mataimakiyar Daraktar harkokin Ilmantarwa da hulda da jama’a ta hukumar Hajiya Hadiza Abbas Sanusi ta rabawa manema labarai, sun hada da na kananan hukumomin Takai, Sumaila, Garko, Albasu, Tudun wada, Bebeji, Doguwa da Karamar Hukumar Garun Malan

Haka kuma sanarwar ta kara da cewa za a gudanar da aikin a Sansanin alhazai na Jihar Kano wato Hajjcamp da misalin karfe Tara na safe

Friday, 19 May 2023

Shugaban EFCC Ya Nemi Cin Hancin Dala Miliyan Biyu Daga Wajena - 1 Gwamna Matawalle

Gwamnan jihar zamfara, Bello Matawalle ya zargi shugaban hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, Abdulrasheed Bawa da neman cin hancin dala miliyan biyu daga gare shi.

Matawalle ya yi wannan zargin ne a wata hira da BBC Hausa a ranar Juma’a, a daidai lokacin da ake ci gaba da takun saka tsakanin gwamnan da hukumar yaki da cin hanci da rashawa.

Idan za a iya tunawa, a wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba, Matawalle ya yi kira ga Bawa ya yi murabus, yana mai cewa yana da tambayoyi da zai amsa kan cin hanci da rashawa.


Sai dai Shugaban na EFCC ya amsa cewa ba shi da wani abin boyewa yayin da ya bukaci Matawalle da ya kai karar hukumomin da suka dace idan yana da wata shaida a kansa.


Duk da haka, da yake magana yayin hirar, Matawalle ya dage cewa ba za a iya amincewa da Bawa ba.


Ya ce, “Ba wai kawai a rika zargin gwamnoni ba ne. Ba gwamnoni kadai ke da baitulmali ba, gwamnatin tarayya ma tana da. Me shugaban EFCC yake yi musu? Kamar yadda yake ikirari yana da hujja akan gwamnoni, bari ya nunawa duniya shedar wadanda ke matakin tarayya.

“Idan ya bar ofis, tabbas mutane za su san shi ba mai gaskiya ba ne. Ina da hujja akansa. A bar shi ya bar ofishin, ina gaya muku a cikin dakika 10 watakila sama da mutane 200 za su kawo shaidar cin hancin da ya karba a hannunsu. Ya san abin da ya nema daga gare ni amma na ƙi.

“Ya nema min cin hancin dala miliyan biyu kuma ina da shaidar hakan. Ya san gidan da muka hadu, ya gayyace ni ya gaya mani yanayin. Ya ce min gwamnoni za su je ofishinsa amma ban yi ba. Idan ba ni da shaida, ba zan faɗi wannan ba. "

Yanzu-Yanzu : Kotu Ta Soke Zaben Zababben Gwaman Jam'iyar LP Alex Otti

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kano, ta soke zaben zababben gwamnan jihar Abia, Dr Alex Otti da daukacin ‘yan takarar jam’iyyar Labour a jihohin Abia da Kano.

Kotun da Mai shari’a M N Yunusa ke jagoranta ta ce fitowar tasu bai bi ka’idojin dokar zabe ta 2022 ba.

An mika kwafin hukuncin da kotun ta yanke ga manema labarai a ranar Juma’a.


Kotun da ta shigar da kara mai lamba FHC/KN/CS/107/2023 da Mista Ibrahim Haruna Ibrahim ya shigar kan jam’iyyar Labour da kuma Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC, ta ce jam’iyyar Labour ta gaza mika rajistar zama mambobinta ga INEC a cikin Kwanaki 30 kafin zabukan firamarensu ya sa tsarin ya zama mara inganci.

“Jam’iyyar da ba ta bi tanade-tanaden dokar zabe ba, ba za a ce tana da dan takara a zabe kuma ba za a iya bayyana ta a matsayin wadda ta lashe zabe ba; saboda haka, kuri’un da aka baiwa wanda ake kara na 1, kuri’a ce ta bata,” inji alkalin.


Idan dai za a iya tunawa INEC ta bayyana Otti na jam’iyyar Labour a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar Abia a ranar 22 ga watan Maris.

Otti ya samu kuri’u 175,467, yayin da Okey Ahiwe na jam’iyyar PDP ya samu kuri’u 88,529. Enyinnaya Nwafor na jam’iyyar matasa (YPP) ya zo na uku.

Yajin aikin likitocin Najeriya ya jefa majinyata a halin kunci


Tarin asibitoci a sassan Najeriya sun fada halin garari saboda karancin likitocin da ke duba marasa lafiya sakamakon yajin aikin gargadin da kungiyar likitoci masu neman kwarewa ta NARD ke yi kasar, inda bayanai ke nuna cewa tuni majinyatan da ke bukatar kulawar gaggawa suka sauya akalar duba lafiyarsu zuwa asibitoci masu zaman kansu sakamakon cunkoson da ake gani a asibitocin gwamnati.


A larabar da ta gabata ne mambobin kungiyar ta NARD suka tsunduma yajin aikin a wani yunkuri na nuna bacin ransu game da rashin cika musu alkawuran da ke tsakaninsu da gwamnati ciki har da karin albashi da akalla kasha 200.

Sai kuma yunkurinsu na kalubalantar kudirin dokar da ke gaban Majalisar kasar da ke shirin kange daga fita ketare don yin aiki har sai bayan sun yi aikin shekaru 5 a cikin Najeriya.

Haka zalika kungiyar likitocin na bukatar gwamnatin Najeriyar ta biya mambobinta bashin kudaden albashin da suke binta tun shekarar 2015 baya daukar tarin ma’aikatan bangaren lafiya saboda karancin ma’aikata a sashen.

Cikin kwana 3 da faro yajin aikin, tuni marasa lafiya suka fara ji a jikinsu saboda rashin likitocin da ke duba lafiyarsu, musamman a biranen da suka kunshi Abuja da Lagos da kuma Kano.

Yanzu haka dai gwamnati Najeriya ta bakin Chris Ngige ta fara tattaunawa da shugabancin kungiyar ta NARD ko da ya ke kungiyar ta musanta.

RFI 

Thursday, 18 May 2023

Ba Ni Da Gida A Kasar Waje - Buhari

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya ce ba shi da gida a wajen Najeriya.

Ya bayyana haka ne a lokacin da yake karbar wasikar girmamawa daga jakadan Birtaniya a Najeriya, Richard Hugh Montgomery da takwaransa na Sri Lanka Velupillai Kananathan a fadar shugaban kasa a ranar Alhamis.

Buhari ya ce “A daya daga cikin ganawarmu da Sarki Charles III, ya tambaye ni ko ina da gida a Ingila, amma na shaida masa cewar ba ni da gida a wajen Najeriya.”

Ya kara da cewa, an shafe shekaru da yawa ana musayar al’adu ta hanyar ilimi da horarwa tare da Birtaniya, inda ya nuna cewa ya samu horon soji a makarantar Mons Officer Cadet da ke Aldershot a Ingila 1962 zuwa 1963.

Buhari ya shaida wa jami’in diflomasiyyar Birtaniya cewa kyakkyawar fahimtar banbance-banbancen al’adu, da mutunta cibiyoyi shi ne ya share fagen yawan nasarorin da Birtaniya ta samu.

Ya ce jami’an diflomasiyyar da suka gabata sun kulla alaka da Sarkin Musulmi, Sarkin Kano, Shehun Borno da Sarkin Ilorin.


Shugaba Buhari ya kuma umarci Montgomery da ya ci gaba da kiyaye kyawawan manufofin diflomasiyya, kamar yadda magabata suka yi, ta hanyar mutunta cibiyoyin gargajiya a Najeriya.

Ya ce dangantakar da ke tsakanin Birtaniya da Sri Lanka za ta kara inganta tare da la’akari da al’adun gida, sarakunan gargajiya, da sauransu.

“Ina jin dadin yadda ake girmama sarakunanmu da hukumominmu, duk da sauyin zamani, ilimi, da karuwar son abin duniya.

“Akwai abubuwa da yawa da za mu koya daga al’adunmu, kuma cibiyoyin gargajiya su ne masu kula da su, kuma ya kamata kowa ya mutunta su,” in ji Buhari.

Ya shaida wa jakadan Birtaniya cewa, huldar diflomasiyyar da ta shafe shekaru da dama tana ci gaba da dorewa bisa mutunta al’adu za ta kara karfi.

A nasa bangaren, Montgomery, ya ce Birtaniya a kodayaushe tana girmama Najeriya da al’adunta, yayin da ya bayyana fatan alheri ga Sarki Charles III, a daidai lokacin da Najeriya ke shirin mika mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2023.

Shi ma a nasa jawabin, jakadan Sri Lanka ya shaida wa shugaba Buhari cewa kasar za ta ci gaba da bai wa sojojin Najeriya kwarewa da gogewa wajen yaki da ta’addanci.
AMINIYA 

El-Rufai Zai Rushe Kamfanoni 9 Mallakar Makarfi

Gwamna Nasir El-Rufai na Jihar Kaduna, ya soke lasisin mallakar kamfanoni tara na tsohon gwamnan jihar, Sanata Ahmed Muhammed Makarfi.

An kuma shirya rushe kamfanoni tara mallakar tsohon gwamnan Jihar.

Aminiya ta fahimci cewa an kai sanarwar janye  hakkin mallaka ga jami’an kamfanonin da abin ya shafa.

Sanarwar ta fito ne daga Daraktan kamfanin rake da ke lamba 11 a Murtala Square, Alhaji Ibrahim Makarfi wanda ya mayar da martani da cewa, “lauyoyinmu za su mayar da martani kan kwace hakkin mallakar kamfanonin”.

Sai dai da yake mayar da martani kan soke hakkin mallakar a wani sakon da ya aike wa Sanata Makarfi, ya tabbatar da samun wasikun soke kamfanonin har guda tara.

Ya ce, “Akwai babban batu. Muna bukatar ganawa da Ustaz Yunus (SAN) domin mu garzaya kotu don dakatar da gwamnatin jiha; kawai sun aiko mana da takardun soke mallaka guda tara”.

Daga cikin kadarorin da abin ya shafa sun hada da filaye guda biyar a Mogadishu, filaye uku a kan titin Kwato, da fili daya a Doka.

A cikin takardun soke hakkin mallakar da magatakardar hukumar kula da bayanan kasa ta Kaduna (KADGIS) ya sanya wa hannu, Mahmud Aminu ya ce, “An umarce ni da na sanar da ku cewa mai girma Gwamnan Jihar Kaduna a cikin ikon da aka ba shi a karkashin sashe na 28 (5) (a) da (b) na dokar amfani da filaye ta 1978, ya kwace hakkin mallakar wadannan kadarori da aka ambata”.

AMINIYA 

Hajj2023 : Hukumar NAHCON Ta Kaddamar Da Tawagar 'Yan Jaridu

Shugaban Hukumar Alhazai ta Najeriya, NAHCON, Alhaji Zikrullah Kunle Hassan, ya kaddamar da tawagar kafafen yada labarai na kasa domin gudanar da aikin Hajji na shekarar 2023 a kasar Saudiyya.

Taron ya gudana ne a ofishin da ke Abuja ranar Alhamis.

Hassan ya jaddada mahimmancin bin ka'idojin ƙwararru, gami da daidaito a aikin jarida.

Ya taya ‘yan tawagar murna da aka zabo su, ya kuma bukace su da su dauki kansu a matsayin abokan hadin gwiwa da NAHCON wajen gudanar da aikin Hajji ba tare da wata matsala ba.

Shugaban hukumar ya bayar da tabbacin cewa za a kwashe dukkan maniyyatan da suka yi rajista a jirgi a kan lokaci, inda ya ce jami’an NAHCON za su tafi kasar Saudiyya ranar 21 ga watan Mayu domin yin shirye-shiryen da suka dace.

Ya nanata kudurin hukumar na tabbatar da cewa alhazai sun samu kimar kudinsu kuma an dauke su cikin gaggawa.

Da yake magana kan da rawar da kafafen yada labarai ke takawa, shugaban NAHCON ya yi kira ga kungiyar kafafen yada labarai ta kasa da su bayyana Musulunci da Hukumar da kyau.

Ya bukaci goyon bayansu, hadin kai, da kuma gaggauta bayar da rahoton duk wani jinkirin da aka samu a hidimar, inda ya bukace su da su tuntubi NAHCON kafin su buga bayanai a yanar gizo.

Sheikh Suleman Mommoh, kwamishinan tsare-tsare, bincike, kididdiga, bayanai, da kuma ayyukan dakunan karatu, ya taya tawagar yada labarai murna tare da jaddada muhimmancin bayar da rahotanni masu inganci da daidaito.

A nasa bangaren, Kwamishinan Ma’aikatar Kula da Ma’aikata da Kudi, Alhaji Nura Hassan Yakasai, ya bayyana bukatar da ke akwai na samar da rahotanni na hakika da ke fifita muradun Musulunci, Nijeriya, da kuma NAHCON.

Alhaji Mousa Ubandawaki mataimakin daraktan yada labarai da yada labarai na NAHCON ya baiwa ‘yan jarida muhimman bayanai game da ayyukansu na sana’a a kasa mai tsarki tare da yi musu fatan Alheri.

Wednesday, 17 May 2023

Labari da dumiduminsa : Tinibu Zai Zo Kano Domin Bude Ayyuka - Ganduje

Gwamnan jihar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana cewa ana sa ran zaɓaɓɓen shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu zai zo jihar kano domin bude wasu aiyuka da gwamnatinsa gudanar a nan kano.

 
” A yayin da muka cigaba da bude wasu daga cikin aiyukan raya kasa da gwamnatinmu ta yi a kwarya birnin kano da kewaye, Muna sa rana Zaɓaɓɓen Shugaban kasa Asiwaju Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano domin kaddamar da sabuwar gadar da muka Samar a kofar mata zuwa Ibrahim Taiwo Road”.


Kadaura24 ta rawaito Ganduje ya bayyana hakan ne yayin da yake jagorantar taron majalisar zartarwar ta jihar kano na wannan makon a gidan gwamnatin jihar kano.


Ganduje yace ya bude aiyuka Masu tarin yawa Kuma zai cigaba da bude aiyukan don raya kasa da gwamnatinsa ta gudanar.

Ganduje dai ya na bude aiyukan da ya gudanar ne a wani bangare na bankwana ga al’ummar jihar kano sakamakon karewar wa’adin gwamnatin sa a ranar 29 ga watan mayu.

An faɗa mana ƙarasa ayyukan da wasu suka faro babbar nasara ce - Zaɓaɓɓun gwamnoni

 


An faɗa wa zaɓaɓɓun gwamnonin da za a rantsar ranar 29 ga watan Mayu a Najeriya, cewa a cikin nasarar shugabanci, akwai ƙarasa ayyukan da magabatansu, suka faro.

Matakin zai taimaka wajen tabbatar ci gaban ƙasa da alkinta dukiyar al'umma da rage kashe kuɗi wajen gudanar da harkokin mulki a matakan jihohi.

Wannan jan hankalin, na cikin ɗumbin bayanai da shawarwari da aka gabatar wa zaɓaɓɓun gwamnonin Najeriya, yayin wani taron sanin makamar aiki da aka shirya musu a babban birnin ƙasar, Abuja.

Manufar taron na kwana uku, ita ce shirya gwamnonin masu jiran gado da dabaru da hikimomin shugabanci kafin a rantsar da su nan da kwana 12.

Ƙungiyar gwamnoni ta Najeriya ce ta shirya taron a Abuja, inda ta gayyato ƙwararru a fannoni daban-daban game da sanin dabarun shugabanci a ciki da wajen ƙasar domin bunƙasa ƙwarewar sabbin gwamnonin.

Jiga-jigan 'yan siyasa kamar Simon Lalong na jihar Filato da Nasiru El-rufa'i da su Kayode Fayemi sun ja hankalin zaɓaɓɓun gwamnonin da za su hau karagar mulkin jihohi su fifita muradan al'umma a kan bambancin siyasa da ta aƙida.

Haka zalika, an ja hankalin sababbin gwamnonin kada su yi ƙasa a gwiwa wajen koyon dabaru da salon ayyukan raya ƙasa daga wasu jihohi, don hanzarta ci gaban jihohinsu.

Ɗaya daga cikin mahalarta taron, zaɓaɓɓen gwamnan jihar Sokoto, Alhaji Ahmed Aliyu ya ce horon sanin makamar aikin, ba shakka zai taimaka wajen inganta gudanar da harkokin mulki a jihohi da zarar sun fara aiki.

Ya ce "kusan in ce mun koma aji. Don aji ne ake shiga tun bakin ƙarfe 9 na safe zuwa 9:30, wata ran a kai ƙarfe 4 ko 5 na yamma".

A cewar Ahmed Aliyu, duk da yake ya yi mataimakin gwamna tsawon shekara huɗu, kuma ya sha gudanar da ayyukan da gwamna ke yi, amma ya koyi sabbin dabaru da bai taɓa samu ba a baya.

"Musamman an nuna mana muhimmancin ƙarin hanyoyin samun kuɗin shiga a jihohinmu.

Kuma an ja kunnenmu game da buƙatar kammala ayyukan da gwamnoni masu barin gado suka faro, saboda da kuɗin jihohinmu ake yinsu", in ji zaɓaɓɓen gwamnan na Sokoto.

A ranar 29 ga watan Mayun nan ne, za a rantsar da su, bayan zaɓen gwamnoni a ranar 18 ga watan Maris.

Governors Induction

ASALIN HOTON,BIODUN OYEBANJI/FACEBOOK

Zaɓaɓɓun gwamnonin za su jagoranci jihohinsu ne tsawon shekara huɗu mai zuwa.

Taken horon “Shugabanci Don Ganin Tasiri: Gina Matakan Mulki a Ƙasa” na da burin ƙarfafa gwiwar sabbin gwamnonin wajen lalubo mafita ga matsalolin da za su fuskanta.

A cewar ƙungiyar gwamnonin ƙasar (NGF) wata manufar taron ita ce faɗakar da sabbin gwamnonin irin girman nauyin da zai rataya a wuyansu na amanar talakawa da kuma hanyar da ta fi dacewa su bi wajen sauke wannan nauyin.

Daraktan watsa labarai na ƙungiyar ta NGF, Abdurrazak Barkindo ya ce da ma an saba gudanar da taron don sanar da zaɓaɓɓun gwamnoni da waɗanda suka ci zaɓe wa'adi na biyu game da wahalhalun rayuwa da mutanensu ke ciki da kuma hanyoyin da za su tunkari matsalolin.

Governors Induction

ASALIN HOTON,GOV AA SULE/FACEBOOK

Abdurrazaƙ Barkinɗo ya ce yayin taron ana tafka muhawara da gabatar da maƙaloli da kuma musayar ra'ayoyi da gogayya da wasu fitattun shugabanni da suka yi mulki.

A cewarsa, ƙungiyar ta gayyato ƙwararru daga cikin Najeriya waɗanda suka haɗar da tsoffin gwamnoni da wasu ƙwararru da masana daga ƙasashe kamar Kenya da Amurka da sauransu.

Governors Induction

ASALIN HOTON,SENATOR UBA SANI/FACEBOOK

Governors Induction

ASALIN HOTON,SENATOR UBA SANI/FACEBOOK

Bayanan hoto,

Sanata Uba Sani, zaɓaɓɓen gwamnan jihar Kaduna shi ma yana halartar taron sanin makamar

Ko da yake, galibi wannan horon ya karkata ne kan yadda za a haɓɓaka tattalin arziƙi da kyautata shugabanci a matakin jihohi, akwai matsaloli da dama shimfiɗe a ƙasa cikin jihohin da sabbin gwamnonin za su karɓi ragamarsu nan da 'yan kwanaki.

Kamar dai na rashin tsaro da kantar talauci da rashin aikin yi da dimbin bashi da kuma rashin biyan hakkokin ma’aikata masu ci da wadanda suka yi ritaya da dai sauransu.

Governors Induction

ASALIN HOTON,ZAYYANU ZAKARIYA GUSAU/FACEBOOK

Bayanan hoto,

Zaɓaɓɓen gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal Dare da Gwamnan jihar Yobe Mai Mala Buni


BBC

Tuesday, 16 May 2023

Abun Da Tinibu Da Kwankwaso Suka Tattauna A Kasar Waje


Shugaban kasa mai jiran gado, Bola Tinubu ya yi wata ganawar sirri da dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Kwankwaso a kasar Faransa.

Wata majiya mai tushe ta ce Tinubu ya yi wa Kwankwaso tayin tafiya tare da shi a sabuwar gwamnati da kuma duba yiwuwar sulhu tsakaninsa da Gwamnan Kano mai barin gado, Abdullahi Ganduje.

A ranar Litinin, mako biyu kafin Tinubu ya karbi rantsuwar fara aiki, suka shafe sama da awa hudu suna ganawar sirrin da Kwankwaso a birnin Paris na kasar Faransa.

Majiyarmu ta ce a yayin ganawar, Tinubu ya bukaci hadin kai domin aiki tare da Sanata Kwankwaso — wanda ya lashe kuri’un Jihar Kano a zaben 2023.
Kwankwaso da shugaban kasar da ke jiran rantsarwa nan da mako biyu masu zuwa sun kuma amince za su ci gaba da tattaunawa kan wannan batu.

Majiyar ta ce mai dakin Kwankwaso da zababben Sanata Abdulmumini na Jam’iyyar NNPP ne suka raka madugun Kwankwasiyya zuwa wurin ganawar.

A bangaren Tinubu kuma, matarsa, Sanata Oluremi da Mataimakin Shugaban Majalisar Wakilai mai barin gado, Femi Gbajabiamila, ne suka raka shi.

Majiyar ta ce “Matar Tinubu, Sanata Oluremi ce ta karbi bakuncin Hajiya Hafsa, a yayin da ‘yan siyasar kuma suka dauki tsawon lokaci suna tattauna a kan hadin kan kasa da abubuwan da sabuwar gwamnati za ta ba wa muhimmanci.

“Sauran sun hada da batun shugabancin Majalisar Dokoki ta Kasa da kuma aniyar zababben shugaban kasan na kafa gwamnatin hadin kan kasa da ake fatan damawa da Kwankwaso a ciki.

“Sun kuma yi waiwaye a kan kawancensu na siyasa tun suna lokacin da suke Majalisar Dokoki ta Kasa a shekarar 19992,” in ji majiyar.

Majiyar ta kara da cewa a yayin zaman an kuma fara tunanin sasanta tsakanin Kwankwaso da tsohon mataimakinsa, wato Gwamnan Kano mai barin gado, Abdullahi Ganduje.

A shekarar 2015 Ganduje ya gaji kujerar Kwankwaso, amma ba da jima ba daga baya suka raba gari, kuma har yanzu ba sa ga-maciji.
AMINIYA 

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

Head of Service Urges Civil Servants to Uphold Ethical Conduct

The Head of Service, Kano State, has called on civil servants to strictly adhere to the Civil Service ethical code and show grea...