Hadakar Jam'iyyun Siyasa A Kano Sun Kauracewa Zanga-zangar Matsin Rayuwa Da Ake Shirin Yi

Jam’iyyar NNPP mau mulki da na adawa da suka haɗa da APC da PDP a unguwar Dakata, Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jihar Kano sun haɗa kai wajen kauracewa zanga-zangar da ake shirin yi kan matsin rayuwa a fadin kasar nan.

Jam’iyyun, ta bakin ciyamonin su na ƙaramar hukumar, sun yi kira ga al’umma da su kauracewa shiga zanga-zangar.

A wani taron gangami da aka yi a Dakata Gidan Dagaci a jiya Asabar, Sabo Sambo (NNPP) da Umar Usman Usman (APC) da na PDP sun gargadi matasa akan illar da zanga-zangar ka iya haifar wa.

A cewar su, akwai sauran hanyoyi da kundin tsarin mulkin ƙasa ya bayar domin neman hajji da yanci daga gwamnati sama da zanga-zanga.

Sun nuna cewa gwamnatin jihar Kano da ta taraiya gana daya shekarar su daya akan mulki, inda su ka kira al’umma da su yi musu uzuri.

“Musamman ma idan aka yi duba na tsanaki za a ga cewa gwamnatin Tinubu da ta jihar Kano, a shekara ɗaya da su ka yi a mulki, sun yi abubuwan yaba wa.

“Za ku ga cewa a bangaren aiyukan lafiya da ilimi da noma duka gwamnatocin sun yi abun yaba wa.

“Saboda haka muna kira gare ku da ku gujewa shiga wannan zanga-zanga wacce ka iya haifar da wata matsalar daban,” in ji su.

Daily Nigeria Hausa

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki