Posts

Shugabannin hukumar alhazai ta kasa (NAHCON) sun kai ziyarar ta'aziyya ga Mangal

Image
LABARI CIKIN HOTUNA Shugaban Hukumar Alhazai ta Najeriya (NAHCON), Alhaji Zikrullah Kunle Hassan, kwamishinan kudi, Alhaji Nura Hassan Yakasai da kwamishinonin ayyuka da wasu ma’aikatan gudanarwa, sun kai ziyarar ta’aziyya ga Shugaban Kamfanin Mangal Group (Max Air) Alhaji Dahiru Barau Mangal a Katsina, bisa rasuwar marigayi Alhaji Bashiru Mangal

MAI MARTABA SARKIN KANO ALHAJI AMINU ADO BAYERO: Baƙon Shehu Maghili

Image
Daga: Magaji Galadima A ranar Litinin 12 ga watan Disamba 2022 gwamnatin Æ™asar Aljeriya ta aiko da wani jirgi na musamman domin ya É—auki mai martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero zuwa Æ™asar ta Aljeriya domin halartar taron duniya na musamman don tunawa da rayuwa da kuma aiyukan shahararren malamin addinin Musulunci sharifi kuma masanin falsafa  wato Shehun malami Muhammad Abdurrahman al-Maghili wanda yayi rayuwarsa tun a Æ™arni na goma sha biyar.  Jigin ya tashi daga Kano da karfe 9:45 na safe. A cikin waÉ—anda suka samu alfarmar raka Sarki wannan tafiya akwai Sarkin Dawakin Tsakar-gidan Kano Alhaji Ahmad Ado Bayero hakimin Kumbotso da Ambasada Ahmad Umar ÆŠanmalikin Kano da Dakta Ibrahim ÆŠahiru Bauchi wanda ya wakilci Sheikh ÆŠahiru Bauchi da Malam Isa Sanusi Bayero da Dakta Lawi Atiku Sanka da kuma ni Magaji Galadima Kachallan Kano, sannan sai wasu malamai da sharifai na Kano da kuma fadawa hadiman Sarki.  Jirgin ya É—an yada zango a Yamai babban birnin Jamhuriyar Nijar inda ya É—auk

Mutane sama da 20 ne suka mutu saboda tsananin sanyi a Amurka

Image
  Fiye da Amurkawa 200,000 ne suka wayi gari ba tare da wutar lantarki ba a safiyar ranar Kirsimeti sakamakon guguwar sanyi da ta shafe kwanaki ana tafkawa a wasu jihohin gabashin Amurka, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutane sama da 20 Matsanancin sanyi, dauke da guguwa mai cike da tarihi ya mamaye  jihohin Amurka 48 a wannan makon, abin da ya haifar da cikas ga matafiya da dakatar da zirga-zirgar dubban jirage, inda dubban gidaje ke cike da dusar kankara. An tabbatar da mutuwar mutane 22 a jihohi takwas, ciki har da akalla mutane bakwai da suka mutu a yammacin New York, inda dusar kankara dauke iska mai tsanani suka mamaye garuruwa. Shugaban gundumar Mark Poloncarz ya shaida wa manema labarai cewa, "Muna da mutane bakwai da aka tabbatar sun mutu sakamakon guguwar da ta afku a gundumar Erie. Wasu ma'aurata a Buffalo, wanda ke kan iyaka daga Canada, sun shaidawa AFP cewa tsananin sanyi ba zai basu damar tafiyar tsawon minti 10 ba na ziyartar danginsu a bikin Kirsimeti. Haka

Dalilin Da Zan Koma Daura Idan Na Bar Mulki —Buhari

Image
Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, ya ce zai koma Daura da zarar ya kammala wa’adin mulkisa don guje wa matsaloli. Shugaban ya bayyana haka ne a ranar Lahadi lokacin da ya karbi bakuncin mazauna Babban Birnin Tarayya don ta su murnar bikin Kirsimeti. Kazalika, Buhari ya gode wa ’yan Najeriya da suka yarda tare da amince masa ya shugabance su. Ya ce duk da ci gaba da aka samu a fasaha da kimiyya, hankalinsa zai fi kwanciya idan ya koma garinsa. Buhari dai ya jima da cewa da zarar ya kammala wa’adin mulkinsa zai bar Abuja gaba daya, don kauce wa shiga sabgogin gwamnatin da za ta gaje shi.

'Ya'yana biyu ne suka rasu saboda cutar Sikila - Buhari

Image
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce 'yayansa biyu ne suka rasu sakamakon cutar Sikila. Buhari ya bayyana hakan ne ranar Juma'a a wajen wani gagarumin taro da 'yan uwa da abokan arziki suka shirya masa kan bikin cikarsa shekara 80 da haihuwa a fadarsa. Yayin da yake jawabi game da rayuwarsa shugaba Buhari ya ce 'ya'yansa biyu ne - da ya haifa tare da matarsa ta farko mai suna Safinatu - suka rasu sakamakon cutar Sikila. Ya ƙara da cewa hakan ya tilasta masa yin gwajin ƙwayoyin halitta a lokacin da ya tashi auren matarsa ta yanzu Aisha Buhari. Ya ce ya dage cewa dole sai matar da zai aura ta kasance tana da ƙwayoyin halitta na AA, don kauce wa ɗaukar cutar Sikila ga 'yayan da zai haifa kasancewar shi yana da ƙwayoyin halitta na AS. Buhari ya auri Safinatu a shekarar 1971. sun kuma haifi 'ya'ya biyar tare da ita.

EFCC Ta Yi Gwanjon Kadarorin Su Diezani A Kasuwa

Image
Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) ta sanar da yin gwanjon wasu kadarorin da ta kwace daga hannun ’yan siyasa da ’yan kasuwa ga ’yan Najeriya masu bukatar saya. Hukumar ta ce kadarorin dai na jibge ne a Jihohin Legas da Ribas da Abuja da Anambra da Gombe da Ebonyi da Kaduna da Delta da Edo daKwara da Kuros Riba da Osun da kuma Oyo. Aminiya ta gano cewa daga cikin kadarorin har da na tsohuwar Ministar Man Fetur ta Najeriya, Diezani Allison-Madueke, wadanda hukumar ta ce an mallake su ta haramtacciyar hanya. A wata sanarwar da hukumar ta wallafa ranar Asabar, EFCC ta ce daidaikun mutane da kuma kamfanoni da kungiyoyin da ke son sayen kayan da aka yi gwanjon dole ne su kasance ba a taba daure su ba a baya. A cewar sanarwar, ga masu bukatar sayen kadarorin, za su iya cike fom din neman saye da za a iya samu a shafin hukumar na www.efcc.gov.ng, kafin daga bisani a gayyace su don ganin kadarorin da ido. Kadarorin da aka yi gwanjon nasu sun hada da wani gida a rukunin gidaje na Herit

’Yan Najeriya Na Kushe Ni Duk Kokarina —Buhari

Image
  ’Yan Najeriya Na Kushe Ni Duk Kokarina —Buhari Shugaba Buhari ya ce ba zai yi kewar shugabancin Najeriya ba saboda kushe shi da ’yan kasar ke yi duk kokarinsa. Buhari ya bayyana hakan ne a liyafar da ’yan uwa da abokan arziki suka sirya masa don taya shi murnar cikarsa shekaru 80 da haihuwa a Abuja, inda ya ce ’yan Najeriya na raina duk fadi tashin da yake kan kasar, don haka ba zai yi kewar mulkar ta ba idan wa’adin mulkinsa ya cika. “Abubuwan da zan yi kewar su a matsayina na shugaban kasa a gwamnatance ba su da yawa, saboda raina kokarina da ’yan Najeriya ke yi a kodayaushe. “Ina iya bakin kokarina, amma wasu na ganin za su iya tsoratar da ni don su samu yadda suke so,” in ji shi. Da yake amsa tambayar ’yan jarida kan jita-jtar da ake yadawa cewa ba shi ne Buharin da ’yan kasar suka sani a baya ba, Buhari ya ce yana sane da hakan, sai dai sanin cewa ’yan Najeriya mutane ne masu son raha ya sa bai damu ba. Ya ce wannan batu ba abin dariya ba ne saboda wasu ne ke kokarin amfani da h

#hajj2023 Hukumar alhazai ta Kano, ta yi kira ga duk mai niyyar zuwa Hajin bana, da ya gaggauta biya

Image