Posts

Akwai yiwuwar a soma cire tallafin fetur a watan Afrilu - Gwamnatin Najeriya

Image
  Akwai yiwuwar gwamnatin tarayyar Najeriya ta soma cire tallafin man fetur daga Afrilun 2023, wato watanni uku kafin yadda ainahin lokacin da aka yi niyyar cire tallafin a baya. Ministar kuÉ—i da kasafi Zainab Ahmed ce ta bayyana haka a wata hira ta musamman da ta yi da gidan talabijin na Arise a yayin wani taro na tattalin arzikin duniya a Switzerland. "Abin da ya fi shi ne wannan gwamnatin watakila ta soma cire tallafi a farkon zango na biyu na wannan shekara saboda zai fi nagarta idan aka cire a hankali a maimakon a jira a cire shi baki É—aya," in ji ministar. Ta bayyana cewa duka Æ´an takarar shugaban Æ™asar Najeriya a lokutan yaÆ™in neman zaÉ“ensu duk suna da ra'ayin cire wannan tallafin Bayan Æ™ara wa'adin watanni 18, gwamnatin tarayya ta shirya kashe naira tiriliyan 3.35 kan tallafin mai daga Janairu zuwa Yunin 2023. Wannan Æ™arin wa'adin da aka yi ya janyo muhawara matuÆ™a kan irin kuÉ—in da za a kashe sakamakon ana ganin cewa zai Æ™ara giÉ“i a kasafin kuÉ—i wanda kum

Duk Mai Son Mukami A Gwamnanatina Sai Ya Kawo Akwatinsa Lokacin Zabe - Atiku

Image
Dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya ce duk dan jam’iyyar da ke neman kwagila ko mukami a gwamnatinsa, sai ya nuna sakamakon zaben mazabarsa kafin a ba shi. Atiku ya bayyana hakan ne ranar Laraba a Abekuta babban birnin Jihar Ogun, yayin taron ganawa da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar. Atiku ya ce halartar kowanne yakin neman zaben jam’iyyar ba shi ne tabbacin samun matsayi ko kwangila a gwamnatinsa ba, jajircewa wajen ganin an kawo akwatinan mazaba ne. Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar ya kuma ce, “Dukkanku magoya bayan PDP ne, kuma kuna so ta dawo mulki, don haka ina rokonku ku tabbatar kun kawo akwatinan mazabunku. Yawon zuwa yakin neman zaben kafatanin ’yan takarar jam’iyya ba shi ne zai sa ka samu aiki ko matsayi ko kwangila ba idan an ci zabe, hanyar da kadai za ku samu shi ne nuna min sakamakon zaben mazabarku. “Kuma ina bai wa kowanne dan takarar PDP umarnin yin hakan, domin da haka ne kadai za mu ci zabe. Atiku ya kuma yi alkawarin farfado

Kotu A Kano Ta Daure Alkalai Kan Badakalar Kudin Marayu Naira Miliyan 99

Image
Wata Kotun Majistare mai lamba 14 a Jihar Kano ta aike da wasu alkalai da ma’aikatan Hukumar Shari’a gidan gyaran hali saboda zarginsu da wawure Naira miliyan 99. Aminiya ta ruwaito cewa Kotun, karkashin Mai Shari’a Mustapha Sa’ad Datti ta aike da mutanen ne bisa zargin su da yin sama da fadi da kudaden wadanda mallakin wasu marayu ne. Tun da farko dai Hukumar Karbar Korafe-korafe da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano ce ta gurfanar da wasu alkalai da kuma ma’aikatan Hukumar Shari’ar Musulunci a gaban kotun. Wadanda aka gurfanar a gaban kotun sun hada da Sani Ali da Sani Uba Ali da Bashir Baffa da Gazzali Wada da Hadi Tijjani Mu’azu da Alkasim Abdullahi da Yusuf Abdullahi da kuma Mustafah Bala. Sauran sun hada da Jaafar Ahmad da Adamu Balarabe da Aminu Abdulhadi da Abdullahi Sulaiman Zango da Garba Yusuf da Bashir Ali Kurawa da kuma Usaina Imam. Takardar karar ta bayyana cewa ana tuhumar alkalan da ma’aikatan shari’ar da laifin hada kai da cin amana da satar Naira m

Ma'aikatan BBC Hausa Da Dama, Sun Ajiye Aikinsu

Image
Akalla ‘yan jarida tara na Sashen Hausa na BBC a Najeriya sun yi murabus a cikin wata daya da ya gabata a wani abin da aka bayyana da cewa ba a taba yin irinsa ba a tarihi  Akalla ‘yan jarida tara na Sashen Hausa na BBC a Najeriya sun yi murabus a cikin wata daya da ya gabata a wani abin da aka bayyana a matsayin wanda ba a taba ganin irinsa ba a tarihin kafafen yada labarai na duniya. Aminiya ta gano cewa ma’aikatan da abin ya shafa sun hada da manyan ‘yan jarida guda biyu, ’yan jarida uku na kafafen sada zumunta – biyu daga cikinsu manyan ‘yan jarida ne – babban mai ba da rahotannin harsuna biyu na Hausa/English Africa, mai ba da rahotannin kafafen yada labarai da kuma ‘yan jaridar bidiyo guda biyu. An tattaro cewa yayin da biyar daga cikin ‘yan jaridar suka bar watan Disambar da ya gabata; Sauran hudun sun yi murabus ne a ranar Litinin din da ta gabata don shiga sabon sashen Afirka na Rediyo da Talabijin na Turkiyya (TRT) a Istanbul. “Wannan lamari ba a taba ganin irinsa

Kuskuren Shekara 24 Ne Ya Jefa Najeriya Halin Da Ta Ke Ciki — Kwankwaso

Image
Dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce kuskuren da shugabannin baya suka yi a shekaru 24 da suka shude ne ya jefa Najeriya cikin tsaka mai wuyar da ta ke ciki a yanzu.  Tsohon Gwamnan na Jihar Kano, ya bayyana haka ne a Landan yayin da yake amsa tambayoyi a ‘Chatnam House’ game zaben Najeriya na 2023. ’Yan takarar Gwamnan Kano sun rattaba hannu a kan yarjejeniyar zaman lafiya Dattijuwar da ta fi kowa tsufa a duniya ta rasu tana da shekara 118 A cewarsa, “Za mu iya alakanta kowane irin abu da ake zargin su ne ke da alhakin halin da muke ciki, tun daga annobar Kwarona zuwa koma bayan tattalin arzikin duniya da sauransu. “Amma a ni a ganina, mun fada halin da muke ciki ne saboda kuskuren da mutanen da aka dora wa alhakin mulkin Najeriya suka tafka a cikin shekaru 24 da suka gabata.” Kwankwaso wanda kuma tsohon Ministan Tsaron Najeriya ne, ya lissafa manyan matsaloli da kasar nan ke ciki da suka hada da rashin tsaro, talauci, rashin aikin yi, h

LABARI CIKIN HOTUNA : Tawagar NAHCON A yayin Zaman tattaunawa da Kamfanin sanya Jari na KIDANA A Makka

Image

Idan Mijina ya Gza bayan Shekara hudu, Ka da ku Sake Zabarsa - Matar Tinubu

Image
  Mai dakin dan takarar Shugaban Kasa na jam ’ iyyar APC, Sanata Oluremi Tinubu, ta shawarci  ’ yan Najeriya da kada su sake zaben mijinta a karo na biyu idan ya gaza tabuka komai bayan shekara hudu. Oluremi ta yi wannan kira ne a wajen gangamin yakin neman zaben Tinubu/Shettima na matan shiyyar Kudu maso Gabas wanda ya gudana a Owerri, babban birnin Jihar Imo. Ta ce, “A ajiye batun addini a gefe, ni Kirista ce. Ko kun taba tunanin cewa wata rana za a samu ‘yan takara Kirista da Kirista? “Me ya kamata ya zama madogara? Tun da mun jarraba ‘yan takara Musulmi da Kirista, bari mu jarraba wannan ma mu gani sannan bayan shekara hudu idan ba su tabuka komai ba kuna iya yin waje da su,” in ji ta. Ta kara da cewa, bai kamata addinin mutum ya zama abin damuwa a sha’anin zabe a Najeriya ba, maimakon haka kamata ya yi a yi la’akari da tsoron Allah da dan takara ke da shi. Saboda a cewarta, “Idan ana da mutum mai tsoron Allah, ba wai Kirista ko Musulmi ba, amma dai mutum mai tsoron Allah. Idan mai

Mun Kashe $1bn Wajen Kwato Yankunan Da ’Yan Ta’adda Suka Mamaye – Buhari

Image
Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, ya ce Najeriya ta kashe sama da Dala biliyan daya wajen sayen makaman da ta yi amfani da su wajen yaki da ’yan ta’adda tun 2015. Buhari ya bayyana haka ne ranar Talata sa’ilin da yake jawabi a wajen Babban Taron Zaman Lafiya na Afirka na 2023, da ya gudana a birnin Nouakchott, Jamhuriyar Musulunci ta Murtaniya. Shugaban wanda aka karrama da lambar yabo ta “Karfafa Zaman Lafiya a Afirka” a Abu Dhabi, ya ce akwai bukatar a rungumi dabi’ar karrama juna da mutuntawa a makarantu, musamman kuma a tsakanin matasa. Haka nan, ya yi kira ga shugabanni da su bai wa rayuwar matasa muhimmanci ta hanyar horar da su sana’o’in hannu domin maganin zaman kashe wando. Cikin sanarwar da ya fitar ta hannun mai magana da yawunsa, Femi Adesina, Buhari ya ce dole a ba da himma wajen hana ta’ammali da kananan bindigogi da sauran makamai a cikin al’umma. Kana ya bukaci yayin taron kasashen Afirka na gaba, a dauki matakin lalubo hanyar magance matsalolin da ke ci gaba

Kotu Ta yi Sammacin Emefiele kan badakalar Dala Miliyan 53

Image
Babbar Kotun Abuja ta sammaci Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Godwin Emefiele, a kan ya bayyana gabanta ranar Laraba dangane da shari’ar sama da Dalar Amurka miliyan 53 na kudaden ‘Paris Club’. A wata kara da aka shigar gaban kotun ranar 20 ga watan Oktoban 2022, Alkalin kotun, Mai Shari’a Inyang Ekwo ya bai wa Emefiele odar ya bayyana a gaban kotun ran 18 ga Janairu don sauraron shari’ar. Umarnin kotun ya biyo bayan karar da lauya Joe Agi, ya shigar ne kan kamfanin Linas International Ltd da Ministar Kudi da CBN ta hannun lauyoyinsa, Isaac Ekpa da Chinonso Obasi. A cikin karar, yana neman kotu ta bai wa Sufeto-Janar na ‘Yan Sanda odar cafke Emefiele da lauyoyinsa tare da gabatar da su ga kotu.K Karar ta taso ne kan hukuncin Dala miliyan 70 da aka yanke wa Linas kan ayyukan lauyoyi game da kudin Paris Club, wanda aka ce Emefiele ya saki Dala miliyan 17 sannan Dala miliyan 53 sun makale. A ranar 23 ga Janairu, 2020 kotu ta yanke hukuncin cewa dole Emefiele ya bayyana “

'Yan Najeriya Miliyan 25 na cikin barazanar yunwa a Shekara ta 2023

Image
Wani rahoton Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana cewa, kusan ‘yan Najeriya miliyan 25 zasu fuskanci bala'in yunwa tsakanin watannin Yuni zuwa Agustan wannan shekara ta 2023, muddin ba a dauki matakin gaggawa ba. Adadin dai kari ne kan mutane miliyan 17 da ke cikin hadarin gamuwa da yunwar a Najeriya wanda aka yi hasashe tun a can baya. Sanarwar da Hukumar Bunkasa Ilimin Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya ta fitar a shafinta, ta ce, rikice-rikice da matsalar sauyin yanayi da tashin farashin kayayyakin abinci, su ne ummul-haba’isin jefa ‘yan Najeriyar cikin kangi yunwa. Sanarwar ta ce, an gaza samar da abinci a jihohin Borno da Adamawa da Yobe da ke yankin arewa maso gabashin Najeiya sakamakon tashe-tashen hankula, ga kuma hare-haren ‘yan bindiga a jihohin Katsina da Sokoto da Kaduna da Benue da kuma Niger. Alkaluman da Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Najeriya NEMA ta fitar sun nuna cewa, matsalar ambaliyar ruwa da aka gani a bara, ta lalata sama da kadada dubu 676  na